Posts

Showing posts from March, 2020

RAHOTON BBC HAUSA DANGANE DA MALAM ZAKZAKY A GIDAN YARIN KADUNA

Image
Hatsaniya a gidan yarin Kaduna inda ake tsare da El-Zakzaky Mintuna 12 da suka wuce —BBC Hausa. Sheikh El-zakzaky na tsare a hannun gwamnati tun 2015 Wasu fursunoni da ke babban gidan yarin Kaduna sun tayar da yamutsi inda suka bukaci gwamnati ta sake su saboda fargabar kamuwa da coronavirus. Rahotanni dai sun ce an yi yamutsin ne bayan wasu fursunoni sun nemi a sake su suna masu ikirarin cewa wasu fursuna biyu sun mutu sakamakon coronavirus. Sai dai shugaban gidan yarin Sanusi Mu'azu Dan-Musa, ya shaida wa BBC cewa batun mutuwar fursunonin ba gaskiya ba ne. A babban gidan yarin na Kaduna ake tsare da shugaban kungiyar 'Yan Uwa Musulmi ta Islamic Movement in Nigeria Sheikh Ibrahim Zakzaky da mai dakinsa. Rahotannin sun ce 'yan sanda sun rika harbi a iska da kuma rufe hanyoyin shiga gidan yarin domin hana fursunonin tserewa. Hakan ya sa kungiyar ta 'Yan Uwa Musulmi, a sanarwar da kakakinta Ibrahim Musa ya aike wa manema labarai ta yi kira ga dukkan hukum

ADDU'AR DA JAGORA (H) YA BAYAR MU RIƘA KARANTAWA

Image
ADDU'AR DA JAGORA (H) YA BAYAR MU RIKA KARANTAWA AKAN AZZALUMAI. اَللّهُمَّ اِنَّ ظُلْمَ عِبادِکَ قَدْ تَمَکَّنَ فى بِلادِکَ حَتّى اَماتَ الْعَدْلَ وَ قَطَعَ السُّبُلَ وَ مَحَقَ الْحَقَّ وَ اَبْطَلَ الصِّدْقَ وَاَخْفَى الْبِرَّ وَاَظْهَرَ الشَّرَّ وَاَخْمَدَ التَّقْوى وَ اَزالَ الْهُدى وَ اَزاحَ الْخَیْرَ وَ اَثْبَتَ الضَّیْرَ وَ اَنْمَى الْفَسادَ وَ قَوَّى الْعِنادَ وَ بَسَطَ الْجَوْرَ وَ عَدَى الطَّوْرَ اَللّهُمَّ یا رَبِّ لا یَکْشِفُ ذلِکَ اِلّا سُلْطانُکَ وَ لایُجیرُ مِنْهُ اِلّا امْتِنانُکَ اَللّهُمَّ رَبِّ فَابْتُرِ الظُّلْمَ وَ بُثَّ جِبالَ الْغَشْمِ وَ اَخْمِدْ سُوقَ الْمُنْکَرِ وَ اَعِزَّ مَنْ عَنْهُ یَنْزَ جِرُ وَاحْصُدْ شَاْفَةَ اَهْلِ الْجَوْرِ وَ اَلْبِسْهُمُ الْحَوْرَ بَعْدَ الْکَوْرِ وَ عَجِّلِ اللهُمَّ اِلَیْهِمُ الْبَیاتَ وَ اَنْزِلْ عَلَیْهِمُ الْمَثُلاتِ وَاَمِتْ حَیوةَ الْمُنْکَرِ لِیُؤْ مَنَ الْمَخُوفُ وَ یَسْکُنَ الْمَلْهُوفُ وَ یَشْبَعَ الْجایِعُ وَ یُحْفَظَ الضّایِعُ وَ یَاْوَى الطَّریدُ وَ یَعُودَ الشَّریدُ وَ یُغْنَى الْفَقیرُ وَ یُجارَ الْمُسْتَجیرُ وَ

SUNANA EL'ZAKZAKY- Anharbeni da matata da 'ya'yana da yayata mai shekara saba'in

Image
Ina zaune cikin gidana tare da iyalaina da wasu daga jama'ana, da misalin karfe 10:30 na daren ranar Asabar 12/12/2015 kawai na ji karar harbin bindiga a unguwata. Na tambaya mene ne? Aka ce wai Sojojin Nijeriya ne suka kawo hari gidana, sun tsaya a nisan kamar kilo mita guda da gidan, suna kashe duk wanda suka gani a kan layin da ke zuwan gidan nawa. Can suka dan tsaya da harbin, sai wani a cikin mutane na, yace a bashi su je su tattauna da Sojojin nan ko za su ji takamaiman dalilin da ya kawo su suke harbi ba tare da sun wa kowa magana ba. Bayin Allah hudu daga mutanen da ke gidana suka tunkare su da nufin jin ko me ya kawo ko? Sai kawai suka bude musu wuta suka kashe su. Daga nan suka cigaba da kisa ba kakkautawa tun wannan farko daren har zuwa wayewar garin Lahadi. Sojojin suka karu a yawa da makamai da Asubahin ranar Lahadi, bayan sun kashe duk jama'ar da ke gidana, suka sakawa gidan wuta ya kwana har ranar Litinin yana ci, gidan ya kone kurmus a yayin da ni da iya

WANI BAƘON AL'AMARI DA YA KUSA YA FARU A ƘASAR IRAN DUK DA HALIN DA DUNIYA TAKE CIKI

Image
Wani bakon abu ya so ya faru a Iran cikin wannan mawucin halin. - A ranar 23 ga wannan watan na Maris ne hukumar dake kula da yada labaran kasar Iran (IRIB) ta fitar da wàni faifan bidiyo wanda a ciki aka hasko hoton wani jirgin yaki kirar F-18 Jet Fighter ya doso kasar Iran gadan gadan,inda irgin ya sato hanya ta tekun Gulf zai bullo ta gabashin kasar.  Wannan lamarin ya faru ne a ranar 20 ga wannan watan na Maris. Ganin haka ne yasa sashin sojan Iran dake kula da tsaron sararin samaniyar kasar suka kintsa domin kaddamar da aikinsu kan wannan bakon jirgin. Amma bisa tsarin tsaro na jumhuriyar musulumci,sai da aka yi masa gargadi sau uku,sannan sai aka bayyana masa cewar ya fa shiga hatsari domin yana tsallakawa Iran zai ji shi a kasa,sai jirgin yayi wuf ya juya ya tsere. - Haka zalika har an seta jirgin za'a harba masa wasu makamai masu linzami, amma sai ya taki sa'a ya dauki gargadin da aka yi masa ya tsere abinsa. Har yanzu Iran bata fito ta nuna kasar da ta turo

SAIDA MALA'KA JIBRILU YANEMI IZININ MANZON ALLAH RANAR DA YAFARA SAUKAR MASA DA WAHAYI

Image
"Mala'ika Jibrilu sai da ya nemi Izinin manzon Allah ranar da ya fara kawo mashi sako,ba makure shi yayi ba" -Shaikh Yakubu Yahaya Katsina. Daga Auwal Isa Musa. A cikin Jawabin da Malamin Addinin Musuluncin nan a 6angaren 'yan uwa Musulmi almajiran Shaikh Ibraheem Yaqoub Alzakzaky na Katsina, Shaikh Yakubu Yahaya ya gabatar a ranar Lahadin nan na tunawa da ranar Yaumul-mub'ath wato ranar da aka fara aiko manzon Allah(S) da Sako zuwa ga Talikai,Malamin yace; Mala'ika Jibrilu(A.s) bai ta6a razana manzon Allah(S) balle makureshi ko kuma wahalar da shi ba tun da yake zuwa kawo masa sako,bilhasali ma yana neman izininsa ne a duk lokacin da yazo garesa. Malamin ya kara da cewa; a lokacin da Manzon Allah ya kai shekara Arba'in. sai Allah ya turo mala'ika Jibrilu da sakon Annabta da Ayar nan ta 'Ikra'a,amma da yazo ya sami Manzon Allah a kogon Hira sai da ya nemi izin shiga wajensa,ba matse shi yayi ba:  "Wata ruwayar a falke (Jibrilu) ya

TAƘAITACCEN TARIHIN SHEIKH YAQUB YAHYA KATSINA

Image
Tarihin Shaikh Yakubu Yahaya Katsina A Takaice. Da sunan Allah mai Rahma mai Jinkai. Tsira Da Amincin Allah Su Kara Tabbata Ga Fiyayyen Halitta, Manzon Tsira Da Iyalan Gidansa Ma'abota Shiriya Da Shiryarwa. Garin, Shekara Da Wajen Da Aka Haifi Shaikh Yakubu Yahaya Katsina. An haifi Shaikh Yakubu Yahaya Katsina a ranar 15 ga watan Rajab,1376 Hijiriyya (1955 Miladiyya) a Unguwar Adoro da ke gab da Unguwar-madawaki a tsakiyar birnin Katsina. Mahaifansa. Maihaifinsa Alhaji Malam Yahaya, haifaffen  karamar hukumar Rimi ne ta Jihar Katsina. Malama Maryam, mahaifiyarsa, 'yar asalin karamar hukumar Mani din Jihar Katsina ce. Ita 'ya ce ga Malam Zubairu, shi kuma Malam Zubairu da ne ga Malam Aliyu, dukansu haifaffun Karamar hukumar Rimi ta jihar Katsina ne. Iyalansa. Yanzu haka Shaikh Yakubu Yahaya yana da Mata biyu da 'ya'ya shatakwas: Tara Maza, Tara Mata. Ya aurar da guda Tara (tsakanin Maza da Mata), Yanzu Saura guda Tara. Karatunsa. A farkon farawa Malamin y