DDALILIN DA YASA MUKA CE AKORI SHARI'AR DA AKE MA MALAM ZAKZAKY(H)

 Abin da ya sa muka nemi a

kori shari’ar da ake wa

Malam [H] – Barista Ishak

Adam

Barista Ishaka Adam na cikin Lauyoyin da

ke tsaya wa Shaikh Ibraheem Zakzaky a

karar da gwamnatin Jihar Kaduna ta shigar

da shi shekaru biyu da suka gabata. A

cikin wannan hirar da suka yi da Aliyu

Saleh, fitaccen Lauyan ya bayyana

dalilansu na shigar da bukatar kotu ta yi

watsi da shari’ar da ake yi wa Shaikh

Zakzaky da maidakinsa Malama Zeenah.

Sannan ya bayyana abin da suke fatan

samu a hukuncin da kotun za ta yanke

ranar Talata 29 ga Satumba mai zuwa.

ALMIZAN: Masu karatu za su so sanin

abin da ya sa Lauyoyin Shaikh Zakzaky

suka shigar da kara suna neman kotu ta yi

watsi da shari’ar da ake yi masa wacce

aka kwashe sama da shekaru biyu ana yi?

BARISTA ISHAKA ADAM: Sakamakon

gwamnatin Jihar Kaduna ta shigar da su

Malam Zakzaky kara tana tuhumar su da

aikata wasu laifuffuka guda takwas tun a

watan Yuni na 2018, wanda aka fara shiga

kotu a ranar 5 ga wata, har ya zuwa yanzu

fiye da shekaru biyu ke nan su Lauyoyin

gwamnatin, ko kuma gwamnatin Jihar

Kaduna ba ta iya kawo shaida ko guda

daya ba. Don haka muna iya cewa har

yanzu ba a fara ‘case’ din ba.

A bangare guda kuma sai muka ga an yi

wa ’yan’uwan da aka kama a waki’ar

Zariya, wadanda aka kama a Disamba,

2015 an yi masu irin wadannan tuhume-

tuhumen, kotu ta wanke su, ta ce ba su

aikata wadannan laifuffukan ba, kuma ta

ma sake su. An saki ’yan’uwa kusan 170,

court 6, 8, 11 (wacce yanzu ta zama court

9), duk sun saki ’yan’uwa, sun wanke su,

sun ce ba su aikata wadannan laifuffukan

ba.

Sannan kuma ga shi kuma sun kasa kawo

shaida. Har yanzu ba su kawo hujja ko

guda daya ba, duk da kuwa suna da su a

rubuce. Sai muka fahimci suna amfani da

abin da ake kira ‘delay tactics’ ne, suna jan

lokaci saboda su kansu sun san ba su da

‘case.’ Don an taba yin wata takwas ba a

ce komai a kan kes din ba, lokacin da aka

tura Alkalin ya tafi kotun sauraron

kararrakin zabe. Ya yi kusan wata shida,

ya dawo ya tafi hutun wata daya, da aka

tashi sanya kes din aka sanya wajen wata

daya.

Wani abin da nake so ka lura da shi ne, su

’yan’uwan da aka wanke ana tuhumar su

ne da cewa sun aikata laifi, su kuma su

Malam ana tuhumar su ne da laifin

ingizawa a aikata laifin. Lokacin da kotu ta

wanke wanda ake zargi da aikata laifi, ina

kuma ga wanda ake tuhuma da ingizawa?

Ka ga shi ma ke nan bai aikata ba. Ka ga

ana rike da shi ne ba tare da ya aikata

wani laifin ba. Wannan kuma ya sabawa

wasu sassa uku na dokokin kasa na tsare

mutum ba tare da ya aikata laifin komai

ba.

Sannan kuma daga cikin dalilin da ya sa

muka bukaci kotu ta yi watsi da wadannan

tuhume-tuhumen akwai cewa ba a dauki

jawabin wanda ake kara ba wanda ake kira

‘taking plea’. Idan ana tuhumar mutum da

laifi ana karanta masa tuhume-tuhumen,

sai a ji ra’ayinsa, zai amince, ko kuwa zai

nuna rashin amincewarsa (guilty or not

guilty). Don haka tunda ba a yi ba, a

shari’a mutum bai san laifin da ya sa ake

tsare da shi ba. Ke nan ana rike da shi ne

ba tare da an sanar da shi dalilin da ya sa

ake tsare da shi ba.

ALMIZAN: Amma Barista a baya an yi wani

abu mai kama da haka, kuma har su

Malam sun nuna ba su aikata laifin da ake

zargin sun aikata ba.

BARISTA ISHAKA ADAM: An yi ‘taking plea’

ne a lokacin da wadanda ake tuhuma da

aikata laifin mutum hudu ne, wato su

Malam da Malama da Malam Yakubu

Yahya da Dakta Sunusi Abdulkadir,

sakamakon an yi gyara a takardar

tuhumar aka cire sunan mutum biyu,

Malam Yakubu Yahya da Dakta Sunusi

Abdulkadir, sai ya zama ana tuhumar su

Malam ne da Malama. Wannan gyaran da

aka yi ya sa wancan ‘taking plea’ din da

aka yi ya riga ya rushe. Yanzu a doka ba a

yi ‘taking plea’ ba. Don haka shi ma

wannan a shari’a wata madogara ce da za

ta iya sa a nemi kotu ta yi watsi da kes

din.

Sannan kuma laifin da gwamnatin Jihar

Kaduna take tuhumar su Malam da

aikatawa, laifuffuka ne wadanda ‘Penal

Code’, wato kundin dokokin shari’ar

laifuffuka na Jihar Kaduna bai san da su

ba, domin an kafa su ne a shekarar 2017,

su kuma su Malam ana tsare da su ne tun

2015. Don haka ka ga ke nan laifuffukan

da ake tuhumar su Malam da aikatawa,

kotun shari’ar laifuffuka na Jihar Kaduna

bai san da su ba. Tsarin mulkin kasar nan

ya ce bai kamata a tuhumi mutum da laifin

da shari’a ba ta san shi ba.

Bisa wadannan hujjojin ne na cewa kotu ta

wanke ’yan’uwa da ake tuhumar su da

tuhume-tuhume iri daya da su Malam,

sannan kuma ga shi sai jan kafa suke, sun

kasa tsayawa a yi kes din saboda sun san

ba su da kes da kuma rashin daukar

jawabin wadanda ake tuhuma (taking

plea), bisa wadannan dalilan ne ya sa

muka nemi kotu ta yi watsa da waccan

karar.

Bisa wadannan hujjojin da na ambata da

wasunsu ma, shi ya sa aka shigar da

wannan korafi aka ce ana son kotu ta yi

watsi da wadannan tuhume-tuhumen da

ake yi masu ta sake su. An shigar da

wannan karar, an rubuta komai an bai wa

Lauyoyin gwamnati, su ma sun rubuta

tasu takardar rashin amincewa da wannan

bukatar da aka shigar, mu ma mun ba su

amsa na rashin amincewar tasu. An bai

wa kotu. Kowa yana da shi a tsakanin mu.

Don haka kotu ta sanya Juma’ar da ta

wuce a matsayin ranar sauraron dukkan

bangarorin, aka yi abin da ake kira

‘adoption,’ wato kowa ya tsaya gaban kotu

ya bayyana cewa ya shigar da kara, kuma

ya amshi takardar daga abokin shari’ar

tasa, kotu ta tabbatar kowa yana da

wannan takardar, kowa yana da takardun

kowa. Yanzu abin da ya rage kotu za ta

natsu ta duba duk takardun bangarorin

biyu, sai ta yanke hukunci, amma yanke

hukunci, bisa wannan bukatar tamu.

Ba za mu ce ga hukuncin da kotu za ta

yanke ba, amma dai a shari’ance za mu

iya cewa kotu tana da zabi guda biyu; na

farko ko dai ta ce ta gamsu da bukatarmu,

su Malam ba su aikata laifi ba. Don haka

ta yi watsi da duk tuhume-tuhumen da ake

yi masu, ta saki su Malam, ba su aikata

wani laifi ba, don haka ta sallame su. Ko

kuma ta ce a bar Lauyoyin gwamnati su

kawo shaidu a ci gaba da kes din, amma

kila sai ta zo da wasu sharruda, kamar ta

ce ta ba da wasu sharruda ta ce nan da

wani lokaci, ko wata uku suna so nan da

lokaci kaza tana so a gama wannan kes

din. Kes din shekara biyu da wata biyu ke

nan ana yin sa, amma har yanzu ba a ma

fara ba, saboda a doka in har kes ba a fara

kawo shaidu ba, ana iya cewa ba a ma

fara shi ba.

ALMIZAN: Amma Barista wasu za su iya

tambayar cewa a doka za a iya la’akari da

hukuncin da aka yanke wa wani a yi

hasashen hukuncin da za a yi wa wani

alhali ba a fara sauraron shari’arsa ba?

BARISTA ISHAKA ADAM: In da a ce

laifuffukan da ake zargin su Malam da

kuma ’yan’uwan da aka saki sun

bambanta, shi ne ba za a iya la’akari ko

dogaro da cewa an kori kes din ’yan’uwa

ba, amma tunda tuhume-tuhumen iri daya

ne, musamman ita babbar tuhumar

(capital offense) ta cewa an kashe wani da

ake kira Yakubu Dan Kaduna, kuma kotu ta

wanke wadanda ake zargi, don haka zai

zama bata lokaci ne, zai zama su Malam

ba su aikata wannan laifin ba. Kuma

wannan a shari’a ana yin sa, ya faru a kes

daban-daban, wadanda manyan kotuna

suka yi irin wannan hukuncin. Kuma a

tsarin doka ana amfani da hukuncin baya

wajen yanke wani hukunci a gaba. Lauyoyi

suna da hurumin su ce; “Wannan shari’ar

da ake yi mana irin ta ta faru a tsakanin

wane da wane a kotu kaza da kotu kaza,

kuma sun yanke hukunci iri kaza. Akwai

irin wannan hukuncin da wasu kotuna da

suke sa’o’in juna da wannan da kuma

wadanda suka girme ta da suka yi irin

wannan hukuncin.” Irin wannan ya ta faru

inda wata kotu wacce take daidai da

wannan kotun da take shari’ar su Malam

ta yanke hukunci irin wannan, kuma wacce

take sama da ita ma ta yanke irin wannan

hukuncin. Wannan yana daga cikin hujjojin

da muka gabatar a gaban kotu.

ALMIZAN: Jama’a za su so su san

matsayin kotun da ke shari’ar su Malam

da ta kuma wacce ta wanke ’yan’uwa

170?

BARISTA ISHAKA ADAM: Sa’o’in juna ne.

Dukkan su State High Court ne. Zai zama

hukuncinsu kamar wannan kotun ce, High

Court 3 ce ke shari’ar su Malam, su kuma

wadancan High Court 6,8, da 9, sune suka

wanke ’yan’uwa, suka ce ba su aikata

laifin komai ba. Dukkan su High Court ne

na Jihar Kaduna, kuma ko da High Court

ce a Kwara, Lagos, Jigawa ko Kano,

matukar a cikin kasar nan ne, duka abu

daya ne. In da a ce kamar Magistrate ce ta

yi hukunci, wacce tana kasa da High Court,

za su iya cewa wannan ai karamar kotu ce

(Lower Court) ce, ba ta da iko a kanmu,

amma kotunan sa’o’in juna ne, kafinsu

daya da kuma wacce take yayarsu ko

kuma uwa a gare su, wato Court of Appeal,

mun hada da hukuncin da ta yanke irin

wannan wanda ta sallami wanda ake

tuhuma din mun ba su.

ALMIZAN: Me kuke fata daga wannan

kudurin da kuka shigar?

BARISTA ISHAKA ADAM: Muna fatan za mu

yi nasara, domin mun fi su hujjoji. Muna da

hujjoji kashi 95, su kuma suna hujja kashi

biyar. Mun yi masu tambayoyi guda

takwas, daya suka iya amsawa, ita din ma

ba su amsa ta cikakkiya ba.

ALMIZAN: Wane hali Shaikh Zakzaky yake

ciki yanzu ganin cewa an kwashe fiye da

shekara biyu ana abu daya, ba gaba ba

baya, kuma ga shi suna fama da rashin

lafiya?

BARISTA ISHAKA ADAM: Su Sayyid dai

kowa ya san ba su ba da lafiya, kuma

Likitoci sun tabbatar da haka. Kowa ya

san abin da ke damun su da abin da aka yi

masu. Ko da ma a ce ba harsasai a jikinsu,

kashe masu ’ya’ya, ’yan’uwansu na jini da

kuma almajiransu fiye da 1,000 a

gabansu, sun isa sanya masu rashin lafiya,

balle su ma aka harbe su a hannu, kafa,

kafada da kansu, yanzu a kansu akwai

baraguzan harsashi sama da 40, wanda

hakan ya haifar masa da cutar shanyewar

barin jiki na wani lokaci a baya, dama

kuma idonsu daya ya mutu. Don haka

suna cikin wani yanayi na rashin lafiya.

Wannan ya sa muke da karfin gwiwa na

cewa kotu ta za ta kalli bukatarmu ta kori

wannan kes din don su samu su je samu

lafiya.

Kotu za ta iya la’akari da rashin lafiyar da

su Malam ke ciki domin su sallame su don

su je su nemi lafiya, kotun ta san halin da

suke ciki, ta gan su, sun bayyana a

gabanta, an yi maganganu sosai, kotu ta

ga yanayinsu. Akwai lokacin da aka zo da

su Malam kotu, lokacin tafiya Indinya din

nan, har ma jama’in tsaro da ma’aikatan

kotu kuka suke yi saboda sun ga yanayin

da su Malam ke ciki. Ni na ga wani dan

sanda da ma’aikatan kotu suna kwalla.

ALMIZAN: A karshe wane sako kake da shi

ga ’yan’uwa?

BARISTA ISHAKA ADAM: Sakona shi ne

’yan’uwa a ci gaba da addu’a dare da rana

ba kaukkautawa, kuma a ci gaba da yin

abubuwan da ake yi, kamar Abuja Struggle

din nan, kuma duk idan ’yan’uwa suke ya

zama suna masu bin tsari da nizami.

ALMIZAN: Mun gode kwarai.

BARISTA ISHAKA ADAM: Ni ma na gode

kwarai.

Voiceofsheikh@gmail.com

Comments

Popular posts from this blog

TAƘAITACCEN TARIHIN SHEIKH YAQUB YAHYA KATSINA

TAKAITACCEN TARIHI, HAIHUWA DA TASOWAR SHAIKH ZAKZAKY (H)

Cikakken Tarihin Hammad Ibraheem Zakzaky