SHEIKH ZAKZAKY; Bayan kammala jami'a

— Bayan Kammala Jami’a:

Daga: Cibiyar Wallafa da Yaɗa Jawaban Shaikh Ibraheem Zakzaky (H). 

Bayan kammala Jami’a, Shaikh Zakzaky ya cigaba da gabatar da gwagwarmayarsa na yunkurin tabbatar da addinin Musulunci. Tun a shekarar ta 1979 ta bayyana balo-balo cewa akwai wata da’awa da ke kira a komawa tsarin addinin Musulunci. Sai dai tana jami’a ce kawai a tsakanin daliban jami’a, amma a waje ba a san da ita ba.

Ana wannan halin ne, kawai sai ga juyin-juya halin Musulunci na Iran a watan February 1979. Ga wani Malamin addinin Musulunci ya kira mutane zuwa ga komawa nizamin Musulunci, kuma ya fafata tsawon shekaru, har yau gashi ya juya kasar ya kori nizamin kafirci ya tabbatar da na Musulunci. Wannan ya karawa Shaikh Zakzaky da masu ra’ayinsa kwarin guiwa sosai, cewa lallai wannan abin da suke da’awarsa mai yiwuwa ne in har sun dake.

Juyin Musulunci na Iran ya kuma ba da amsa ga masu ganin cewa ba zai yiwu addinin Musulunci ya dawo yai iko da mutane ba, a yayin da ga wani Malami ne, amma ya jagoranci yunkuri har ma ya tabbatar da Musuluncin. ‘Revolution’ din Iran kamar yadda Shaikh Zakzaky ya sha fada, ya kara masa kwarin guiwa sosai a wannan lokacin, cewa abin da suke kira a kai din nan fa mai yiwuwa ne.

— Bayan Juyin Musulunci A Iran

Bayan Juyin Musulunci a Iran, a shekarar 1980 Shaikh Zakzaky ya samu ziyartar Jamhuriyar ta Musulunci ta Iran, inda har yai dacen samun damar ganawa da Imam Khumaini (QS) a lokacin yana gadon asibiti. Imam ya yi musu jawabi, har ma Shaikh Zakzaky ya yi ‘recording’ din jawabin ya yo guzurinsa. Wannan ma ya kara wa Shaikh Zakzaky kwarin guiwa sosai da karin shaukin jin cewa lallai dawowar ikon addini ba abu ne mare yiwuwa ba.

Don haka bayan dawowar Shaikh Zakzaky daga Iran, aka rika shirya lakcoci a jami’o’i yana zuwa yana jawabi a kan abin da ya gani da abubuwan da suka burge shi a jamhuriyar Musulunci ta Iran. Shaikh Zakzaky ya fara da jawabi a jami’ar Lagos, ya je Ibadan, sannan Ilori, sai Jos, sai Maiduguri, yayi a Jami’ar Bayero ta Kano, da jami’ar Sokoto, da sauran jami’o’in Nijeriya. Haka ma a ABU da ya gabatar, mutane sun cika sosai, sun rika zuwa daga wurare mai nisa don sauraron wannan tsarabar.

Comments

Popular posts from this blog

TAƘAITACCEN TARIHIN SHEIKH YAQUB YAHYA KATSINA

TAKAITACCEN TARIHI, HAIHUWA DA TASOWAR SHAIKH ZAKZAKY (H)

Cikakken Tarihin Hammad Ibraheem Zakzaky