Posts

Showing posts from October, 2020

Tuna Baya: SAI YAUSHE LAUYA BAYERO DARI ZAI TUBA YA DENA KARE KARYA!?

Image
 Tuna Baya: SAI YAUSHE LAUYA BAYERO DARI ZAI TUBA YA DENA KARE KARYA!?  Ranar: 2-3 November, 1998 (13-14 Rajab, 1419H) KOMAWA DA SU SHAIKH ZAKZAKY KOTU A KARO NA GOMA: Ranar litini 2 ga Nuwambar 1998 ya kamata a cigaba da shari’ar su Shaikh Zakzaky tare da yan uwa uku; Alhaji Hamid Dallami, Malam Abubakar Almizan da Malam Shittu Muhammad wadanda gwamnatin Abacha ta kai kara tana zarginsu da laifin sun ce "Babu Hukuma Sai Ta Allah." amma sai ya zama ba a kai su kotun ba, ba a kuma yi zaman ba, sannan ba a fadi dalilin hakan ba.   Washegari Talata, 3/11/1998 sai aka kai su Malam din kotu da misalin karfe 11 na safe, amma sai 12:30 na rana Alkali Adamu Kafaranti ya shigo kotun. Nan mai gabatar da kara a ranar, Lauya Bayero Dari ya mike yace su ba a shirye suke da su cigaba da gabatar da karar ba, saboda babbar lauyar Gwamnati, Ann Ishaku ta bukaci ita ce za ta gabatar da karar ba shi ba, kuma wai bata da lafiya. Bayero Dari yace, shi a matsayinsa na karamin lauya bai kamata ya c

TUNAWADA WAƘI'AR ZARIYA 2015

Image
 TUNAWA DA WAKI'AR ZARIYA 2015 — Saifullahi M Kabir  Dukkanmu mun ji cewa a ranar Alhamis, 28 ga Safar 1437, daidai da 10/12/2015, bayan kammala zaman juyayin ranar wafatin Manzon Allah (S), Shaikh Zakzaky ya bayar da sanarwar taron saka tutar Maulud, wanda yace za a gudanar a yammacin ranar Asabar 1 ga watan Rabi'ul Awwal, 1437 (12/2/2015). Wanda a shekarun da suke gabanin wannan shekarar, sojoji sun saba gabatar da bikin yaye sabbin kuratan sojojin a Zariya a duk karshen shekara, a ranar Juma'a da safe. Sai dai a wannan shekarar, sai suka mai da bikin yayen nasu zuwa ranar Asabar 12 ga Disambar 2015, kuma da yammaci, maimako Juma’a da safe kamar yadda suka saba gabatarwa a tsawon shekaru.  Wannan ya ba su damar ya zama rana da lokacin bikin nasu ya yi daidai da na taron sauya tutar Mauludi da Harkar Musulunci ta ayyana za ta gabatar a Husainiyyah Bakiyyatullah a wannan ranar. Harka ba ta yi tunanin dage taronta a wannan ranar ba, ko daukar wani mataki na musamman, ganin c

NASIHAR SHEIKH ZAKZAKY GA 'YAN UWA MASU AMFANI DA KAFAR SADA ZUMUNTA

Image
  NASIHAR SHAIKH ZAKZAKY GA ‘YAN UWA MASU AMFANI DA SOCIAL MEDIA Wannan wata nasiha ce da Jagoran Harkar Musulunci a Nijeriya, Shaikh Ibraheem Zakzaky ya yiwa ma’abota amfani da shafukan sada zumunta (social media) musamman ‘yan uwa Musulmi almajiransa, da cewa; yanzu lokaci ne na Hujja, ba zagi ba. Karatu a bakin masu abin ya fi saurin ganewa. Ga nasiharnan kamar yadda take: “Idan wani ya zana Malaminka, ya sa a ‘internet’, ya sa shi a sifar Biri ko Kare, ba kai kuma sai ka zana nashi Malamin ka ce; kai ma ka ce Malaminshi kaza ba ne, sai ka bar shi da abokanansa (masu zana Annabi a mummunan kama), ya nuna inda ya kwana. Duk wanda zai zana wani Malami, ko da wane ne Malamin, idan ba ka da ra’ayin Ibn Taimiyyah, ba za ka nuna shi a mummunan kama ba ne, za ka ce; Ibn Taimiyyah ya ce kaza, amma ba haka ba ne. Amma ba zagin shi za ka yi ba. Kowane ya ce kaza, ko ya fadi kaza, amma ba haka ba ne. Amma idan su wadannan suka zana Malaminku, a mummunan kama, ko suka zana Ayatullah suka yi mis

YAU SHEIKH TURI YA CIKA SHEKARA 59

Image
  Yau Shaikh Muhammad Turi Ya Cika Shekaru 59 — Saifullahi M. Kabir Yau 15 ga Safar, 1442 tayi daidai da irin ranar da aka haifi Shaikh Muhammad Mahmoud Turi a shekarar 1383Hijiriyya. Shaikh Muhammad Turi, wanda tun yana yaro dan shekara 14 ya hadu da Shaikh Ibraheem Zakzaky, kuma ya sallama masa dari-bisa-dari, ya samu tsananin kauna da soyayya tsakaninsa da Jagoransa, har ta kai ma ga Jagoran ya furta cewa ya ji yana kaunarsa. "Kuma raina ya zauna da Malam Turi tun bayan wata magana da ta gudana tsakaninmu muna kurkuku n Kaduna tare, kuma na ji kaunarsa ya shiga zuciyata. To na ji cewa ba wanda ya kamata lallai ya rike wannan al'amari face Malam Turi, saboda wasu dalilai wanda ba zan bayyana su a nan ba, ba ma zan gaya wa kowa ba." Inji Shaikh Zakzaky (H). Malam Turi, gwarzo ne sadauki, a lokacin Abacha, bayan kama Shaikh Zakzaky, shi ya rika jagorantar yan uwa Muzaharori ba tare da razani ko tsoro ba, har zuwa sadda aka kama su suma. Haka ma ya sha fada cewa duk sadda