Posts

Showing posts from August, 2020

DDALILIN DA YASA MUKA CE AKORI SHARI'AR DA AKE MA MALAM ZAKZAKY(H)

Image
 Abin da ya sa muka nemi a kori shari’ar da ake wa Malam [H] – Barista Ishak Adam Barista Ishaka Adam na cikin Lauyoyin da ke tsaya wa Shaikh Ibraheem Zakzaky a karar da gwamnatin Jihar Kaduna ta shigar da shi shekaru biyu da suka gabata. A cikin wannan hirar da suka yi da Aliyu Saleh, fitaccen Lauyan ya bayyana dalilansu na shigar da bukatar kotu ta yi watsi da shari’ar da ake yi wa Shaikh Zakzaky da maidakinsa Malama Zeenah. Sannan ya bayyana abin da suke fatan samu a hukuncin da kotun za ta yanke ranar Talata 29 ga Satumba mai zuwa. ALMIZAN: Masu karatu za su so sanin abin da ya sa Lauyoyin Shaikh Zakzaky suka shigar da kara suna neman kotu ta yi watsi da shari’ar da ake yi masa wacce aka kwashe sama da shekaru biyu ana yi? BARISTA ISHAKA ADAM: Sakamakon gwamnatin Jihar Kaduna ta shigar da su Malam Zakzaky kara tana tuhumar su da aikata wasu laifuffuka guda takwas tun a watan Yuni na 2018, wanda aka fara shiga kotu a ranar 5 ga wata, har ya zuwa yanzu fiye da shekaru biyu ke nan su

YUNƘURIN ZUBAR DA JINI. yakamata ɗan'uwa yayi kyakykyawan shiri.

Image
 Me Zasuyi Nan Gaba? Allahu A'alamu:-  SABODA HAKA MUTUM YAYI KYAKKYAWAN SHIRI DAGA NAN ZUWA ARBA'EENA—Shaikh Yakubu Yahaya Katsina. "Sai su ce ai dan an tare hanya ne, shin hukuncin tare hanya shi ne ayi ma mutum abinda akayi wa Su Malam? Ko kuma suce ai dan ana zagin sahabbai ne to dama ita gwamnatin ta kare sahabbai ce? Kuma a kawo mana jawabi 1 ko inda jagoranmu Malam Ibraheem Zakzaky (H) ya zagi wani sahabi... Saboda haka su 'yan'uwa kada suyi tunanin ba zasu kara ba, a'a shirye suke su kara, Allah kadai kuma Ya san miye tanadinsu, tunda sunje wata jaha sunyi taro kwanannan taron sirri irin wanda sukayi wancan lokacin wanda suna gama taron suka afka ma Malam a Zariya. To sun kara yin irin wannan taron kwanannan. To kaga mi zasuyi nan gaba Allahu A'alamu, kaga ashe ba bari sukayi ba, ba kuma shirye suke su bari ba. Illa dai kamar yadda nace ta namu bangare din mu dauki 'Ayyi Ihtimal' (Any Possibility) in Allah Ya rayar da mu falillahil hamdu, ya

MUHIMMAN RANEKU 400 A TARIHIN HARKAR MUSULINCI A NIGERIA

Image
 Daga littafin: MUHIMMAN RANEKU 400 A TARIHIN HARKAR MUSULUNCI A NIJERIYA –Saifullahi M Kabir Na: Cibiyar Wallafa Da Yada Ayyukan Shaikh Zakzaky (H) RANAR:15 May, 1984 (14 Shaaban, 1404H): A Ranar Talata, 15 ga watan Mayun 1984 ne wa'adin zaman Shaikh Zakzaky a kurkukun Inugu na kamun gwamnatin Shehu Shagari ya cika. Bayan Malam din ya shafe shekaru uku cur da wata daya a tsare.  An kama Shaikh Zakzaky ne a garin Sokoto a ranar 15 ga watan Mayun 1991, inda wata kutu ta yanke masa daurin shekaru hudu (kamar yadda bayanin kamun ya gabata).  Lokacin da Shaikh Zakzaky ya fito daga wannan kurkukun, isowarsa Zariya ke da wuya ya riske masu tariyarsa wadanda a lokacin 'yan uwa ne kasa da mutum 30. Kuma ya yi musu jawabin karfafawa, akan cewa kar su ga cewa bamu da yawa a yanzu, nasara ba shine yawan mutane ko kafa daula ba.  Malam ya yi bayani cewa, nasara a wajen Allah (T) shine mutum ya koma gareShi yana mai biyayya a gare shi, in ya samu uzuri a wajen Allah ya samu nasara kenan. Ha

LABARIN WANI KARE MAI KISHIN ANNABI MUHAMMAD (S)

Image
 LABARIN WANI KARE MAI KISHIN ANNABI (S.A.W) KARE MA YANA KISHIN FIYAYYEN HALITTU ANNABIN RAHAMA (S.A.W) Babban Malamin nan, Shakundum a fagen ilimin Hadisi, Alhafiz Ibn Hajar Al-asqalani, wanda ya rasu a shekarata (852) bayan Hijra. Babban Malamin ya rawaito a cikin littafinsa mai suna الدرر الكامنة في أعيان المائة الثامنة Littafi ne na (Tarajum) wato littafi ne da ya kunshi tarihin Manyan Malamai, da Manyan Sarakuna, da Shugabanni, da mawaqa masana harshen larabci, wadanda suka rayu tun daga shekara ta dari bakwai da daya (701) har zuwa karshen shekara ta dari takwas daidai (800) bayan hijra, duk Malamin da ya ambaci tarihinsa, sai kuma ya ambaci wani abu da aka rawaito daga gareshi na ruwayoyin Hadisi ko wani labari. Kamar dai yadda Ibn Hajar din yayi bayani da kansa a gabatarwar littafin. Alhafiz Ibn Hajar da yazo tarihin wani Malami mai suna: "Aliyyu Bin Marzuq" sai ya ambaci labarin wani kare mai ban mamaki da ya faru a wajajen shekara ta dari bakwai bayan hijra, yau ku

RANAR MUBAHALA

Image
hrtvnetwork.ng@gmail.com  CIKKEN BAYANI AKAN RANAR MUBAHALA DA ANNABI (S.A.W.W) YAYI DA KIRISTOCI.  Daga Shafin Alwilayah news na malam Awwal Bauchi.  Da Sunan Allah Mai Rahama Ma i Jin Kai ) فَمَنْ حَآجَّكَ فِيهِ مِن بَعْدِ مَا جَاءكَ مِنَ الْعِلْمِ فَقُلْ تَعَالَوْاْ نَدْعُ أَبْنَاءنَا وَأَبْنَاءكُمْ وَنِسَاءنَا وَنِسَاءكُمْ وَأَنفُسَنَا وأَنفُسَكُمْ ثُمَّ نَبْتَهِلْ فَنَجْعَل لَّعْنَةُ اللّهِ عَلَى الْكَاذِبِينَ( “To, wanda ya yi musu da kai a cikinsa, a bayan abin da ya zo kama daga ilmi, to ka ce: “Ku zo mu kirayi ‘ya’yanmu da ‘ya’yanku da matanmu da matanku da kanmu da kanku, sa’an nan kuma mu kankantar da kai, sa’an nan kuma mu sanya la’anar Allah a kan makaryata”. (Suratu Al-Imrana 3:61) Kusan karshe-karshen rayuwar Ma’aiki (s.a.w.a), sakamakon irin nasarar da Musulunci ya samu kuma yake ci gaba da samu, da dama daga dauloli da kasashen da suke kewaye da daular Musulunci sun nufo Madina don mika wuya da amsa kiran Manzo (Musulunci), sai dai duk da haka wasu daga cikin kasashe d

GHADEER MAKOMAR AL'UMA BAYAN WAFATIN MANZON ALLAH(S) Daga Mal. Awwal Bauchi

Image
GHADEER MAFITAR AL'UMMA Ghadir, Makomar Al'umma Bayan Ma'aiki (s.a.w.a): Daga: Muhammad Awwal Bauchi IRIB-Tehran - I.R.of Iran awwalubauchi@yahoo.com  ________________________ Da Sunan Allah Mai Rahama Mai Jin Kai A matsayinmu na musulmi, mun yi imani cewa addinin Musulunci addini ne da aka sauko da shi ga dukkan bil'Adama sannan kuma shari'arsa ta kumshi dukkan abin da dan'Adam yake bukata a rayuwarsa ta yau da kullum. Kamar yadda kuma muka yi imani da cewa gudanar da wannan shari'a da jagorancin al'umma yana hannun wanda yazo da sakon ne wato Manzon Allah (s.a.w.a) matukar dai yana raye, wannan lamari ne da dukkan musulmi suka hadu a kansa. Abin tambaya da kuma kace nacen shi ne yadda lamarin zai kasance a bayansa. Mabiya Ahlulbaiti (a.s) sun yi amanna da cewa ayyana wanda zai gaji Ma'aiki (s.a.w.a) wajen gudanar da wannan aiki nasa ba yana hannun kowa ba ne face Allah da ManzonSa (s.a.w.a), wato a takaice dai al'umma ba su da bakin magana ciki

IBN TAIMIYYA NE JAGORAN ZAGIN SAHABBAI

Image
 IBN TAIMIYYA NE JAGORAN ZAGIN SAHABBAI, KARYATA HADISAN ANNABI MUHAMMAD(SAW), TAJSIM (MAYAR DA ALLAH JIKI)... -  A MAHANGAR KALAMAN AL-BANI, AZ-ZAHABI, IBN HAJAR AL-ASKALANI... MAFI YAWAN SAHABBAI DA TABI'AI MUNAFIKAI. - A MAHANGAR KALAMAN IBN TAIMIYYA: IBN TAIMIYYA ZINDIKI (MARAR ADDINI) NE, MUNAFIKI NE... A MAHANGAR MALAMAN AHLUS-SUNNAH. INJI IBN HAJAR AL-ASKALANI: IBN TAIMIYYA BAI DA AMANAR ILIMI, YA KAN KARYATA HADISAI INGANTATTU... - A MAHANGAR KALAMAN AL-BANI, IBN HAJAR AL-ASKALANI... Al-bani ya tabbatar da Ibn Taimiyya ya kan karyata hadisai ingantattu. Lokacin da Al-bani ya ke ta'aliki akan hadisi ingantacce, mutawaturi (hadisin Ghadir); wanda Ibn Taimiyya ya karyata, sai Al-bani ya ce: "Abin mamaki ne sosai, Ibn Taimiyya ya runtse ido; ya yi inkarin (ingancin) hadisin (Ghadir), har ma ta kai ga ya karyata wannan hadisin, a littafinsa (Minhajus-Sunnah, j 4, s 104), kamar yanda (Ibn Taimiyya) ya karyata hadisin da ya gabace shi [wanda Annabi(saw) ya ke cewa: Ali(as

ABINDA YA FARU A HAJJIN BANKWANA. Sheikh Ibrahim zakzaky(H)

Image
voiceofsheikh@gmail.com LABARIN ABUBUWAN DA SUKA FARU A HAJJIN BANKWANA ZUWA RANAR GHADEER. — Shaikh Ibraheem Zakzaky (H). Manzon Rahma (S) a karshen aikensa, (sakon da ya isar daga wajen Ubangijinsa), bayan ya isar da kusan komai na addini don dama haka Allah (T) ya tsara bisa hikimarSa, isar da sakon Manzon Allah ba gaba daya aka yi ba, a hankali- a hankali aka yi, Manzon Allah kuma yana bayani a hankali- a hankali. Yayin da al’amarin (wannan addinin) ya kusa kamala. Sai Allah ya aiko Manzonsa (Jibrilu kenan) izuwa ga Annabi Muhammad (S), yace masa; ‘Ka isar da duk addini, illa yanzu abu biyu suka rage; Ka yi hajji, ka nunawa Muminai yadda za su yi Hajji, sannan akwai kuma wulaya (wato za ka fada musu wanda za su bi a bayanka), domin yanzu bayan isar da sakonka z aka koma i zuwa ga Ubangijinka.’ Saboda haka sai Manzon Allah (S) ya sa aka yi yekuwa, ba kawai a Madina ba, har a dukkanin sassan (garuruwan) da Muminai suke, duk wanda Allah ya horewa halin zuwa Hajji, to ba a dauke masa b