Posts

Showing posts from April, 2020

TARIHIN SHEIKH ZAKZAKY DAGA BAKIN SA 2

Image
TARIHIN SHAIKH IBRAHEEM ZAKZAKY DAGA BAKINSA (2) — Daga Littafin HARKAR MUSULUNCI Na Cibiyar Wallafa Cigaba.... A lokacin da nake jami’a akwai wani yanayi da na samu, wanda kuma shi ya taimaka wajen canza rayuwata. Lokacin da na shiga (jami’a) kamar kowane dalibi, fatata shine na kammala jami’a wala’alla na je na kama aiki, ko kuma ma na cigaba da karatu a nan jami’a din, to amma yanayin da muka samu kanmu a ciki a wannan lokacin na karshen 70s, kamar za a iya cewa akwai musayar ra’ayi dangane da abin da ya dace ya zama makomar kasa. Lokacin kwaminisanci na tashe sosai, kuma da yawan dalibai da suke nuna sun waye, Kwaminisanci suke yi. Haka suma cikin Lakcarori wadanda suke nuna su cigababbu ne to Kwaminisanci suke. Saboda haka Kwaminisanci kamar shine wata alama ta cigaba. Kuma Kwaminisanci na da matsalar cewa suna ganin addini kamar wani mummunan abu ne. Kuma su kan ta yin hujumi a kan addini baki daya, da kuma musamman ma Muslunci. Suna ta sukan Musulunci, suna nuna kamar

TAURARUWAR AREWACIN NIGERIA-Nana As'ma'u

Image
Tauraruwan Arewacin Nigeria A Qarni Na Sha Tara: Nana Asma'u  Bint Fodio. By Anas Lawal A tarihin ƙasar nan anyi jarumai Maza da yawan gaske amma Mata Kadan ne tarihi ya tuna dasu, a ƙarni na Sha Tara, an samu jajirtacciyar mace, Malama, yar uwa, gimbiya, uwa, kuma marubuciya daga gidan mujaddadi shiekh Usman Dan Fodio (1754-1817) wato Nana Asama'u bnt Fodiyo. Haihuwar Ta An haifi Nana Asama'u ne shekarata 1793/4, shekaru 11 Kafin kafa Daular Sakwkkwato, a garin Ɗegel ga shehu mujaddadi, an haifeta ne a matsayin tagwaye amma Dan uwanta ya rasu tun Suna qanana. Shehu ya sanya mata Suna Asama'u ne Domin tuna Sahabiyyar nan Mai daraja Nana Asama'u bnt Abubakar Saddiq. Nana Asama'u ba fullatana ce yar Qabialar Toronkawa. Gidan Su kuwa gidan Malamai, Abdullahin Gwandu Baffanta  ne Muhammad Bello kuma Yayanta ne Dan Fodio kuma Mahaifinta. Karatun Ta Malama Asama'u tayi karatun addini Mai zurfi  awurin mahaifinta Dan Fodio, da sauran malaman gidansu. Ta

TARIHIN SHEIKH ABUL FATHI MAIDUGURI

Image
Wane Ne Sheik Abul Fatahi Maiduguri? Daga Aliyu Ahmad . Cikakken sunansa shine Sheik Ahmad Aliyu Yarwa amma ana yi masa lakabi da Sheik Abul Fatahi. Ya rayu a duniya shekaru 82, kenan an haife shi a shekarar 1919. Da rasuwarsa yau shekaru 17 kenna, domin ya rasu ne a shekarar 2003. . An haife shi a wani kauye da ake kira Sandiya amma an fi saninshi da Shanduwa a yanzu, a gundumar Konduga ta jihar Borno. A nan ya taso har ya iya hawan doki da al'adun kauye. NASABARSA: Sheikh Ahmad bin Aliyu bin Ahmad bin Aliyu bin Muh'd Mustapha bin Muh'd Mukhtar bin Adam bin Dawud bin Abdulganiyyu bin Zubair bin Abbas bin Hussain bin Suleiman bin Ishaq (ta kan wannan suka hada kaka daya da Sheik Ahmad Tijjani) bin Aliyu Zainul Abideen bin Ahmad bin Muh'd Nafsu-Zakiyya bin Abdullahil-Khamil bin Hasanul-Musanna Bin Hassan bin Aliyu wa Fadima Bintu RASULILLAHI SAW. . Ta bangaren mahaifiya kuwa jikan Yarima Zubairu ne Sarkin Adamawa, sunanta Aishatu bintu Alh Muh'd wa Hauwa'
Image
🌐 *Kauna Da Yanke Kauna* 🌐 Kafin bayyanar Musulunci, dan’Adam dai ya rayu cikin yanayi na jahiliyya mai tsanani cikin karnoni da dama, kafin daga baya hasken Musulunci da shiriyar da Manzon Allah (s.a.w.a) ya zo da ita ta bayyana ta kuma haskaka duniya. A wancan lokacin dai dan’Adam yana rayuwa ne cikin yanayi na dar-dar da yanke kauna, sai dai kuma lokacin da ya ji kalmar ‘yanci daga bakin Mai Albishir, Manzon Allah (s.a.w.a) yana kiransa zuwa ga shiga jirgin ‘yan’Adamtaka, nan take ya bude zuciyarsa, ya kuma karbi wannan kira na kauna da fatan alheri. Haka dai lamarin yake, a duk lokacin da aka samu duhun jahiliyya ya mamaye duniya, al’umma suka yanke kauna da fata, sai a samu wani sako na Ubangiji da zai zo ya yaye wannan duhu daga kan al’umma ya kuma dawo musu da kauna da kuma fatan da suke da shi. *وَ إِنْ مِنْ أُمَّةٍ إلاّ خَلاَ فِيها نَذِيرٌ* *“Kuma babu wata al’umma face wani mai gargadi ya shude a cikinta”.* (Surat Fatir: 24). Haka dai hasken Alqur’ani ya ratsa

Iman Mahdi Al' muntazar

🌐 *Imam Mahdi Al-Muntazar (a.s)* 🌐 Rikici tsakanin alheri da sharri a doron kasa dai ya faro ne tun daga farko-farkon wannan duniya kuma wannan gasa da rikici zai ci gaba tsakanin tafarkuna bbiyn; wato tafarkin shiriya da tafarkin bata; tafarkin Annabawa da tafarkin ma'abota girman kai. Hakika sakon Musulunci ya samu nasara ta hannun Manzon Allah (s.a.w.a) kuma haka wannan tafarki ya ci gaba har ya gina tafarkin tauhidi, ya ciyar da dan’Adam gaba bisa tushen ilmi da imani, ya haskaka shi  da wannan haske kana kuma ya shiryar da shi da wannan shiriya madaukakiya. To sai dai kuma daga baya wannan tafarki ya fara yin rauni, lokacin da wasu akidu da wayewa na jahiliyya suka fara kunno kai, aka fara samun koma baya a wayewa ta Musulunci, aka hana dan’Adam rayuwa karkashin inuwar imani, gaskiya, adalci da zaman lafiya. A bangare guda kuma zalunci ya ci gaba da yaduwa a fadin duniya, al’adun jahiliyya suka fara samun gindin zama, har muminai suka fara yanke kauna, idan da ba don s

TARIHIN SHEIKH ZAKZAKY DAGA BAKIN SA

Image
TARIHIN SHAIKH ZAKZAKY DAGA BAKINSA (1) — Daga Littafin Harkar Musulunci na Cibiyar Wallafa Bismillahir  Rahmanir Raheem. Sunana Ibraheem Zakzaky. An haife ni ne a Zariya an shekara ta 1953 Miladi, wanda yayi daidai da Hijiri Kamari 1372. Mahaifina Malamin Alkur’ani ne, haka ma kakana, shima Malamin Alkur’ani ne, haka ma shima uban kakana. Sai dai shi uban kakana da kuma kakan nawa a lokaci guda suna karantar da karatun littafi irin su Fiqihu da ire-irensu baya ga karatun Alkur’ani. Amma duk cikarsu mahaddata ne, kuma kwararru a kan Alkur’ani din. Kuma har wala yau su kan hada da yin noma a matsayin hanyar rayuwa, baya ga koyar da karatun Alkur’anin. To, haka nan kuma ita ma mahaifiyata, bangaren gidansu suma Malamai din ne. Da yake tsarin rayuwa a wajenmu a da, kusan kowane abu iyali ke yi. Wato akwai wadanda suke sarakai ne, akwai wadanda suke Malamai ne, akwai wadanda kuma ‘yan kasuwa ne. To, ni ta bangaren uwa da ubana duka abin da ya shafi Malinta suke yi. Na’am, akwai

TARIHIN SHEIKH ZAKZAKY (H)

Image
TAKAITACCEN TARIHIN SHAIKH IBRAHEEM ZAKZAKY (H) Daga Cibiyar Wallafa An haifi Jagoran Harkar Musulunci, Shaikh Ibraheem Yaqoub Zakzaky a cikin birnin Zariya, a ranar 15 ga Sha’aban 1372 (May, 1953). Iyayensa Malaman Alkur’ani ne, suna karantarwa da kuma yin noma a matsayin hanyar gudanar da rayuwa. Don haka Shaikh Zakzaky yana tasowa ya fara karatun Alkur’ani a wajen Mahaifinsa. A daidai lokacin da yake karatun Alkur’ani a wajen mahaifinsa, an kuma saka shi a wata makarantar Alkur’ani a lokaci guda, yana zuwa makaranta yana kuma yin karatu a gida. Sannan kuma yana raka mahaifinsa tare da ‘yan uwansa zuwa gona don aiki. A ka’idar gidan su Sayyid Zakzaky a wancan lokacin sai yaro ya sauke Alkur’ani sannan yake saka littafan addini ya karanta a zaurukan Malamai. Don haka lokacin Shaikh Ibraheem Zakzaky yana dan shekaru 14 ya sauke Alkur’ani, nan take ya saka littafai ya fara karatun addini a wajen Mahaifinsa, mahaifiyarsa da kuma wasu Malamai a zaurukansu a cikin birnin Zazzau.

RANAR LAFIYA TA DUNIYA

Image
RANAR LAFIYA TA DUNIYA. Ƙalu bale ga Gwamnatin Nigeriya. Ranar 7 ga watan Afirilun kowace shekara, rana ce da aka kebe domin tunawa da kafuwar hukumar lafiya ta duniya wato WHO a shekarar 1948, kimanin shekaru 72 da suka gabata ke nan. Zaharaddeen Ishaq Abubakar Hukumar lafiya ta Duniya wato WHO tana gudanar da aikace-aikacen ta na jin ƙai aduk faɗin duniya, musamman,ma' ga mata da ƙananan yara domin daƙile yaɗuwar cututtukan da ke bazuwa, bama kamar a yankunan Afrika. Nigeriya tana ɗaya daga cikin ƙasashe masu tasowa da hukamar ta WHO ta maida hankali a kanta duba da yanayin da ƙasar take ciki, na ƙalu balen BokoHaram da yanayin na rikice rikece bama kamar a Arewacin ƙasar. Bincike ya tabbatar da cewa duk'ƙasar da ke fama da yawan faɗace faɗacen Addini ko ƙabilanci, ko kuma halin yaƙi tafi fama da matsalar kiwon lafiya, kasantuwar rashin kwanciyar hankali da bazai bada dama afuskanci ɓangaren lafiyar gadan gadan ba. Nigeriya tana ɗaya daga cikin ƙasashen da suka fi

BARA'A DA WULAYA DAGA SHEIKH IBRAHIM ELZAKZAKY

Image
SHELAR BARA'A DA WULAYA DAGA SHAIKH IBRAHEEM ZAKZAKY (H) A RANAR 5/4/1980 A FUNTUA Da sunan Allah mai murkushe azzalumai. Ya ’Yan uwa Musulmi maza da MATA! Assalamu alaikum wa rahamatullah. An ruwaito cewa Sayyidina Ali Dan Abu Talib (Allah ya yarda da shi) ya ce: “Ya ku mutane, hakika Manzon Allah ya ce; ‘idan wani ya ga wata gwamnati ta mai da zalunci kiranta, ta keta haddodin Allah, ta shuka kiyayya ga sunnar Manzon Allah, tana aikata barna da zalunci a tsakanin bayin Allah, to a wannan hali duk wani wanda bai yi amfani da hannunsa da bakinsa ya yi yaki da wannan zalunci da barna ba, to ya sani fa Allah zai kai shi matsugunin wannan Jagoran gwamnati, ya sa duk cikar su a wuta.” To fa! Ga shi kuwa gwamnatin kasar nan ba ma kawai ta mai da zalunci kiranta bane, a kan zalunci ne aka gina ta; ba ma kawai ta keta haddin shari’ar Allah bane, ta aje shari’a ne waje guda ta dauki shari’ar da mutum ya tsara; ba ma kawai ta karya alkawarin Allah bane, tun farko ma ba ta dauki alka

TARIHIN SHEHI IBRAHIM INYASS

Image
TARIHIN SHEHU IBRAHIM INYASS A HARSHEN HAUSA . Zamu tashi NISBATUN (dangartakarsa ko Alaqarsa da sauran iliman Addini) . 9- NISBATUN (dangartakarsa ko Alaqarsa da sauran iliman Addini):- shine tasawwuf shi kulliya ne acikin ilimai kuma sharadi ne cikin dukkan ilimai, domin babu ilimin ko wani Aiki face da gaskiyar nufi zuwa ga Allah. . Ikhlasi sharadi ne (mai zaman kansa) cikin ilimin ko aiki wannan fassara ce ingatacciya a shari'a ko jiza'i ko lada. . Amma fassara. Ta samuwar. Waje ilimai suna samuwa a waje ba tare da sufanci acikin su ba, sai dai ilimin tauyayyene. . Shiyasa jalaluddeen As suyutiy yace alaqar sufanci da ilimai kamar Alaqar ilmul bayaan ne da ilmun Nahwu. . Wato shine cikar kamalar cikin ilimai, kuma cikar kyawu ga ilimai. . Sheikh zarruq R.A yace Alaqar sufanci da Addini shine Alaqar Ruhi da jiki (idan babu ruhi gangan jiki ya tashi daga aiki) Domin shi tasawwuf muqamul ihsan ne (kyautaye) wanda maulana Rasulillah S.A.W ya fassara jibreel da ce

AMFANI DA SUNAN MIJI BAYAN AURE

Image
AMFANI DA SUNAN MIJI BAYAN AURE Sauya sunan Mahaifi zuwa na Miji, na daga cikin babban kuskuren da Mata ke yi bayan sun yi aure. Shin kun san wannan dabi'a ta sauya sunan Mahaifi zuwa na Miji, haramun ne a addinance? Misali: Kafin auren mace za ka ga sunanta 'Aisha Lawal Isa' amma bayan ta auri 'Ibrahim Yusuf' sai ka ga ta koma 'Aisha Ibrahim Yusuf' ko kuma 'Aisha Ibrahim' kawai. Wannan haramun ne, kuma Musulunci bai yarda mace ta dauki sunan mijinta ta yi amfani da shi ba, a takaice ma dai, wannan dabi'ar ta samo asali ne daga Kafirai, makiya Allah da ManzonSa. A kan wannan, akwai gargadi mai tsanani daga Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallam. Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallam ya ce, "Duk wanda ya danganta sunansa da na wani da ba mahaifinsa ba, Allah zai yi fushi da shi, haka ma Mala'iku da ma dukkan mutane." (Ibn Maajah 2599). Abu Dharr (Allah Ya yarda da shi) ya ce, ya ji Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasall

ƊAURI A MAƘYANƘYASAR ƘWAYOYIN CUTA.

Image
Dauri A Makyankyasar Kwayoyin Cuta Daga Mohammed Ibraheem Zakzaky Duniya ta tsinci kanta a cikin wani irin hali na bullar annobar Coronavirus; cutar da ta haifar da matsanancin tsoro da birkita lamurra. Wannan annobar ta zo da wani salo da ya saba da sauran cututtuka masu yaduwa, tana yaduwa ba tare da bambancewa ko la’akari da bin mugun tsari irin wanda aka yi amfani da shi wurin tsara kisa da batar da wasu ba, ciki kuwa har da ‘yan uwana shida. Gaggawa cutar take yi a lokacin da ta fara mararin kashe wadanda ta rubuta kashewa. Fiye ma da gaggawa irin ta Buhari. Annobar Cutar ta fi kama da irin annobar da za a yi fama da ita a karshen sa’i. Hatta wadanda suke da kololuwa a taka-tsantsan sun tsinci kansu a yanayi na rashin sanin takaimaimen yanayin wannan cuta da yadda za a fuskance ta. Ko da yake da yawan masana a fannin kiwon lafiya sun dukufa wurin nemo rigakafin wannan cuta kafin nan da wasu watanni masu zuwa ko shekara ma; zancen gaskiya dai, wannan hatsari ne da ba a san ko

BIKIN CIKA SHEKARU 40 DA SHELANTA HARKAR MUSULUNCI A NIGERIA

Image
BIKIN CIKA SHEKARU 40 DA SHELANTA HARKAR MUSULUNCI Ranar Lahadi 5 ga watan Afrilun 1980, Jagoran Harkar Musulunci A Najeriya, Shaikh Ibraheem Zakzaky ya fara shelanta Da'awarsa ta tawaye ga duk wani tsari ko doka da ya sabawa na Allah (T) da jaddada wulayarsa ga Allah (T) da tafarkinsa a gaban dandazon al'ummar Musulmi a garin Funtua. Wannan Lahadi din mai zuwa, 5/4/2020 shekaru 40 cur kenan da yin wannan shelar ta Sayyid Zakzaky, wacce ana kaddara ta a matsayin mafarin tafiyar Gwagwarmayar Musulunci a Nijeriya a bayyane. ko da yake kafin wannan ranar, an dauki akalla shekaru uku, Shaikh Zakzaky na yin da'awar a matakin sirri a tsakanin daliban MSS na jami'a. Tarihi ya tabbatar da cewa tun a shekarar 1977 Shaikh Ibraheem Zakzaky ya fara da'awa da kokarin farkar da mutane zuwa ga muhimmanci da wajabcin rayuwa a karkashin ikon addinin Allah (T), ta hanyar shirya lakcoci akan manufar halittar dan adam a doron kasa, muhimmancin fikira, ma'anar kalmar Shahada d