Posts

Showing posts from February, 2021

AYYUKAN NISFU RAJAB

Image
_______________يوم النصف من رجب________________ AYYUKAN YININ 15 GA RAJAB (YAU ASABAR) Yau Asabar ne 15 ga watan Rajab mai girma a kasar Nijeriya. Wannan ranar ne tsakiyar Rajab (Nisfu Rajab) rana mai falala da girma. Akwai ayyuka da aka ruwaito ana yi a wannan yinin, daga cikinsu akwai: 1- An so a yi wanka a wannan ranar na 15 ga watan Rajab Mai Girma. 2- An so a ziyarci Imam Husaini (AS); An samu ruwaya a kan hakan; An tambayi Imam Ridha (AS) cewa; A wace wata  ne zamu ziyarci Imam Husaini (AS)? Sai Imam (AS) yace: “A cikin Nisfu (rabin) Rajab da Nisfu Sha’aban.” 3- Sallah raka’o’i hudu (4); An ruwaito daga Abi Abdullahi (AS) yace; Adiyyu bin Thabit al-Ansary ya shiga wajen Imam Ali (AS) a ranar 15 ga watan Rajab (Nisfu Rajab), Sai ya same Shi (AS) yana sallah……… Bayan ya sallame sai ya daga hannayensa sama, sannan ya karanta wannan addu’ar ta kasa: " أللهم يا مذل كل جبار ويا معز المؤمنين، أنت كهفي حين تعييني المذاهب وأنت بارئ خلقي رحمة بي، وقد كنت عن خلقي غنياً، ولولا رحمتك لكن

Yunƙurin Hana Al'majirci; Ga abinda Sheikh yaqub Yahaya yace...

Image
Kokarin Hana Bara Da Almajiranci: Sakon Sheikh Yakubu Yahaya Ga Gwamnati Sheikh Yaqub Yahaya Daga: Bilya Hamza Dass Sheikh Yakubu Yahaya, sananne Malamin Addinin Islama ne mazaunin garin Katsina, me karantarwa tsawon shekaru, kuma yana daga cikin Almajiran Sheik Ibraheem Zakzaky. Malamin ya aika sako ga hukumomi da Gwamnatoti a kokarin da suke na hana tsarin karantarwa na Almajiranci da Bara, inda ya bayyana ra'ayin shi da kuma yanda yake kallon yakamata ayi, yayi Jawabin ne a wata ganawa da yayi da manema labarai a jihar kwanakin baya. “To abinda muke kallon wannan shine mukaddima na rufe makarantun Allon duk kasar nan baki daya. Domin yanzu abinda gwamnati ke babatu akan shi shine makarantun allo sun dame su da bara basuson bara. Bamuce bara addini ne ya kawota ba, bamuce bara dede ne ba, yin bara ba ba dede bane, amma menene ya sanya musulmi suka zama mabarata? ai da can kasar a hannun su take gidan Mallam ake biyawa aci abinci har a dauka akai gida, da bature yazo y

MAULUDIN IMAM ALI (A.S) A GARIN ZARIYA

Image
MAULUDIN IMAM ALI YA KAYATAR AGRIN ZARIA wajen yanka Al'kakin Birthday Imam Ali  Alhamis 13 ga watan rajab     Wanda yazo daidai da 25 ga February inda aka gudanar da mauludin imam Ali bin abi dalib data gudna a muhalin fudiyya zaria. Anfara maulud din da misalin karfe hudu na yamma inda aka fara da bude taro da addua,kana daga  bisani aka gabatar da display. yan uwa sha'irai ma ba'a barsu bayaba inda sukaita rere baitocin na yabon  Imam Ali. Malam Aminu sakatare shine yazamo bako mai jawabi na farko malamin yayi bayanai masu gamsarwa dangane da janibin imam Ali. Cikin jawabin nasa malamin yanacewa " Imam Ali shine mutun na farko kum shine na karshe da'aka haifa a dakin qa'aba" haka zalika ya cigaba da cewa Imam Ali yayi sharia baa canzata har  a wajen Allah S.W.T Bayan ya kammala ak gabatar da mai jawabi na gaba malam Ibrahim usman na malam Tijjani khalifa zaria. Malamin yafara ne da bada tarihin  imam Ali inda yakecewa " kamar yadda tari

MAULUDIN IMAM ALI A MARKAZIN 'YAN'UWA NA KATSINA @2021

Image
MAULUDIN IMAM ALI (A.S) YA CI GABA A MARKAZ KATSINA. Sheikh Yaqub Yahaya Katsina Daga Bin Yaqub Katsina Yanzu haka Shaikh Yakubu Yahya Katsina na ci gaba da jawabin Mauludin Imam Ali (A.S) da yammacin nan na ranar Alhamis 13,rajab1442 dai dai da 25/2/2021. Bayan mawaka sun gama wakokin yabon Imam Ali (A.S) sai Shaikh Yakubu Yahya Katsina ya ci gaba da jawabinsa. Da farko dai Shaikh ya gode ma Allah bisa wannan babbar ni’ima da Allah yayi ma al’umma da duniya baki daya. Har wa yau Shaikh din ya dora karatunsa na yau ne a kan Kore shubuhar da aka rudi al’ummar Musulmi da ita na cewa; Baban Imam Amirul Mumineen (Ali) ba musulmi ya rasu ba, wato Sayyid Abu dalib. Shaikh ya ci gaba da karyata wannan shaci fadin zance inda yake cewa “Manzon Allah (S) shi ne ya sallaci Abu dalib kuma shi ne mutumin farko da ya fara shaidawa da Annabtar Annabi tun Annabi na karami, (a wajansa)”. Hotunan taron ne muka dauko maku da ke gudana a Sabuwar Markaz Katsina.

DAKARFIN TSIYA AKA NEMI BATAR DA IMAM ALI AMMA BAI ƁATU BA

Image
DA KARFIN TSIYA AKA NEMI A BATAR DA IMAM ALI (A.S) AMMA BAI BATA BA. Inji Sheikh Ibraheem Zakzaky (H) Ga link din da zaku bi mu turo muku videon jawabin https://chat.whatsapp.com/DqxEcgD8udZKgQQIsyc9LT Da karfin tsiya aka nemi batar da imam Ali (As) Amma bai bata ba aka dauki darajijinsa duk aka ba kowa amma duk da haka dai sai da yayi banbaro yafita daban, to yanzu lokacin da Allah yaga daman asan gaskiya ne kuma yaga damar a fada, Na'am har yanzu munajin tsoro akwai abinda bama fada, ba domin munajin tsoron mahukunta ba don su mahukuntan sunce ba ruwan su da addini amma da'ace mahukunta sun tabbatar da addinin da ransu yake so ne ko kayi ko a yanka ka to da shi ne amma yanzu mahukunta sunce ba ruwansu da addini mutum yayi addinin da yaga dama  Na wani hakimi yace ko kyankyaso kake so sai ka bauta mar, tsabar isgili ma yace wannan kazamin kwaron ma yana iya zama uban giji    To ba su mukejin tsoroba tsoron mu shine kar mu gayawa mutum magana domin ya shiriya yazo y

ASALIN ADDU'AR UMMU DAWUD- Daga Muhammad. Suleman Kaduna

Image
ASALIN ADDU’AR UMMI DAWUD DA AKE YI A RAJAB Daga Muhammad Sulaiman Kaduna Ummi Dawuda wata baiwar Allah ce da ta kasance a zamanin Imam Sadik (AS). Asalin sunanta Fadima. Dawud sunan danta ne wanda tare ta shayar da su mama da Imam Sadik (AS), kasantuwar a lokacin, Larabawa suna da al’adar kai ’ya’yansu raino zuwa ga wasu mata. Misali kamar yadda Halimatus Sa’adiyya ta raini Manzon Allah (SAAW). Dawud yana daga cikin jikokin Imam Hasan (AS). To, Halifan Abbasawa na lokacin mai suna Mansur ya sa aka kamo wasu daga cikin jikokin Imam Hasan da ke zaune a Madina a kawo su zuwa Irak. To, daga cikin wadanda aka kamo akwai shi wannan Dawud din. Da aka kai su Irak, aka wuce da su zuwa kurkuku, aka tsare su har lokaci ya tsawaita ba a sako su ba.  Wani lokaci, Ummi Dawud ta ji labarin cewa, an kashe su, wani lokaci kuma ta ji labarin cewa suna raye. Ummi Dawud ta dukufa da addu’a, kuma ta sa bayin Allah dabam-dabam da su taimaka mata da Addu’a kan wannan al’amari. Tana cikin wannan

Shekara 1 da yin wannan jawabin: fitowar 'yan'uwa daga kurkuku ba zai sa mu manta da abinda akai mana ba

Image
Shekara 1 Da Wannan Jawabin ! Fitowan 'Yan'uwa Daga Kurkuku Ba Zai Sa Mu Manta Da Abinda Aka Mana Ba.     Inji Sheikh Adamu Tsoho Jos Insha Allah nan da wani 'dan lokaci muna da sika muna da tsammanin Allah zai kawo mana karshen wannan jarrabawa na fitowan Jagoranmu Sayyid Zakzaky (H). Duk da cewa sun kashe darurukan Almajiran Malam, kuma har yanzu suna kan yi, Alhamdulillah a ranar Alhamis sun saki sauran 'yan'uwa da suka kama tun lokacin wakiyar Zariya. Kuma a yankin Jos akwai mutane 4 da suka kasance cikin wanda aka saka. Duk da yake muna magana ne akan Sayyida Fatima (As), abinda zamu yi koyi da Fatima (As) shine jajircewa ta tsayu ta sadaukar da rayuwan ta bata ji tsoron kowa ba. Duk abinda aka mata bai sa taji tsoron kowa ba, tayi tsayin daka wajen kare jagorancin Imam Aliyu (As). To, dan haka hakki ne muyi koyi da ita wajen kare hakkin Malam (H). Abinda ya faru da Malam wajibin mune mu sadaukar da rayuwan mu da dukiyan mu wajen kare Malam. Wannan

LOKACI MUHIMMIN ABU NE GA RAYUWAR DAN ADAM

Image
LOKACI MUHIMMIN ABU NE A RAYUWAR DAN ADAM Inji Shaikh Adamu Tsoho Ahmad A yayin da yake tsokaci dangane da cikarsa shekaru 59, a jiya Lahadi a wajen Mauludin Amirulmuminin (AS) a garin Jos, Shaikh Adamu Tsoho Ahmad ya bayyana cewa: “A lokacin da ake murnar tunawa da ranar haihuwa, bayin Allah kuma kan tuna da cewa ajalinsu na kara kusantowa ne.”  Yace “Kamar yadda Imam Khumaini ya kawo cewa, da zaran mutum ya kai shekaru 37 ake kammala siffar halittarsa, da ya cika 40 shikenan ya kammala cika mutum, hankalinsa ya kammalu, daga nan zai rika baya ne a komai, ciki har da ji da ganinsa, da kuma karfin jiki.” Shaikh Adamu yace, rayuwar mutum na da iyaka, kuma iyakan nan ne lokaci, lokaci yana da muhimmanci, shi yasa ma Allah (T) ya rantse da lokaci a Alkur’ani mai girma. Ya cigaba da cewa: “Lokaci ya kasu uku; dazu, wanda ya wuce, imma ya zama hujja a gareka ko a kanka. Sannan akwai yanzu, wanda shine naka, ana mafani da shi wajen shiryawa dazunka. Sannan akwai anjima, wanda shi

HOTUNAN MAULUDIN SAYYIDA ZAHRA A KATSINA KASHI NA 2

Image
Wannan sune kashi na biyu na hotunan Bikin Mauludin Sayyida Zahra da aka gudanar a katsina Lahadi 21/2/2021-9/7/1442