Posts

Showing posts from December, 2019

AL'MAJIRAN SHEIKH ZAKZAKY 38 GWAMNATIN BUHARI TA KASHE ACIKIN SHEKARAR DATA GABATA 2019

Image
ALMAJIRAN SHAIKH ZAKZAKY 38 JAMI’AN TSARO SUKA KASHE A SHEKARAR 2019 Daga Saifullahi M. Kabir A yayin da shekarar Miladiyya ta 2019 ke karewa a yau Talata, muna tunawa da irin ta’addancin gwamnatin Buhari a kan ‘yan uwa Musulmi almajiran Shaikh Zakzaky (H), wanda ya sabbaba samun Shahidai akalla 38 a cikin wannan shekarar. A ranar 9/7/2019 ne ‘yan sanda suka bude wuta a kan masu muzaharar kira a saki Shaikh Ibraheem Zakzaky, inda suka kashe mutane biyu a kofar majalisar tarayyar Nijeriya a garin Abuja. ‘Yan uwan da suka kashe a wannan ranar sune Shahid Jafar Mika’il Lafiya da Shahid Mahmud Umar Suleja. Bayan kwana uku da wannan waki’ar a ranar 11/7/2019 kuma ‘yan sanda suka kuma budewa masu muzahar kira a saki Shaikh Zakzaky din a garin Kaduna, inda suka kashe ‘yan uwa Musulmi guda biyu; Shahid Ahmad Nasir da Shahid Abubakar Aliyu Badikko. Kwanaki biyar bayan hakan, a ranar Talata 16/7/2019 ‘yan sanda suka kuma aukawa masu muzaharar kira a saki Malam Zakzaky a Kaduna, inda su

TAKARDAR SANARWAR MANEMA LABARU AKAN BATUN SHEIKH ZAKZAKY(H)

Image
TAKARDAR SANARWAR MANEMA LABARAI *BATUN SHAIKH ZAKZAKY BA A HANNUN GWAMNA EL-RUFA’I YAKE BA* Muna so mu bayyana karara tare kuma da yin watsin baro da kalaman Antoni-Janar na Gwamnatin Tarayya kuma Ministan Shari’a na kasa, Abubakar Malami SAN na cewa batun Jagoran Harkar Musulunci a Nijeriya, Shaikh Ibraheem Zakzaky da mai dakinsa Malama Zeenah, batu ne wanda yake a hannun gwamnatin Jihar Kaduna da kuma Gwamnan Jihar, Nasiru Ahmed El-rufa’i. Ba za a iya taba yaudarar mu ba da kowane irin salon makirci na nuna cewa wannan gwamnatin ta Muhammadu Buhari ba ta da hannu a cikin batun auka wa Shaikh Zakzaky da kuma ci gaba da tsare shi. Da farko, ba wani abin da akwai shakku a kai ba ne cewa gwamnatin tarayyar Nijeriya ita ce ta kaddamar da kisan kiyashin Zariya wanda aka yi a cikin watan Disamba, 2015, lamarin da ya sabbaba kisan ’yan’uwa Musulmi na Harkar Musulunci a Nijeriya sama da mutum dubu daya haka siddan, tare kuma da kamawa da tsare Jagoran Harkar Musulun

SAKON JAGORAN JUYIN JUYA HALI NA IRAN.

Image
Sakon Jagoran Juyin Juya Hali Na Kasar Iran Sayyid Khamne'i Kan Bikin Haihuwar Annabi Isa (AS) ....... Shafin twitter na Ofishin Jagoran juyin Musulunci a Iran ya mika sakon taya murna kan zagayowar bukukuwan Kirsimeti ga dukkanin mabiya addinai da aka saukar daga sama. A cikin sakon Jagoran, ya bayyana cewa: "Kauna da girmamawa da Musulmi suke yiwa Annabi Isa Almasihu (AS) bai gaza wanda mabiya addinin Kirista suke yi masa ba". Jagoran ya isar da makamanciyar irin wannan sako a harshen Farisanci wanda ya kunshi dogon jawabi. Shafukan isar da sakon Jagora da harsunan Turanci, Larabci, Faransaci, Hausa, da dai sauran manyan yaruka na diniya sun fassara da wadan nan yauruka domin sakon ya isa ga masu jin wadan nan yaruka.

PRESS STATEMENT

PRESS STATEMENT *SHEIKH ZAKZAKY’S FATE NOT IN THE HANDS OF EL-RUFA’I* We wish to categorically repudiate the audacious insinuations by the Attorney-General of the Federation (AGF) and Minister of Justice, Abubakar Malami SAN that the fate of the leader of the Islamic Movement of Nigeria, Sheikh Ibraheem Zakzaky and his wife, lies in the hands of the Kaduna state government and its governor, Nasiru Ahmed El-Rufai. We are not deceived by any denial of complicity of General Buhari-led Federal Government. Firstly, the Federal government’s criminal complicity in the heinous genocide in Zaria of December, 2015 that led to the extrajudicial murder of over a thousand members of the Islamic Movement in Nigeria and the subsequent arrest and detention of the Sheikh is beyond doubt. This much was accepted and testified to by the General himself in an interview he granted a Qatari Television Channel while on a visit there as early as March 2016. The Saudi Crown Prince’s self-confessions dur

ZANTUKAN HIKMA DAGA BAKIN SHEIKH ZAKZAKY (H)

Image
[12/29, 6:03 AM] Ysf Hamisu Sani: "Mu makamanmu na hankali ne, muna magana muna rubutu, su kuwa suna sa hauma-hauma da zage-zage da harbi da kamu da dauri. Sai mu ce idan da da gaske in in kuna iyawa mu komo fage daya, na hankali da ilimi, ku fada mu fada, ku rubuta mu rubuta, a kaima al'umma talla ta zabi daya. Sun san a nan ba za su yi nasara ba, don haka sai suke saka bindiga. To bindiga tana da iyaka, sun kuma yi 'mistake' wajen sa bindigar, saboda da basu sa ba ma tun asali, da sai su rika ba da tsoro da bindigar, suce zan harbe ka! To sun harban, me Kuma ya rage? Yanzu za su bamu tsoro da me kuma? Akwai abin da kuke da shi bayan bindiga? In akwai ta ku harba. Iyakanta kenan ma (bindigar), da ita ce aka nemi a bamu tsoro kuma bamu ji tsoron ba, kuma bamu jin tsoron." — Shaikh Ibraheem Zakzaky a bikin shekaru 25 da Harka Islamiyya. [12/29, 6:04 AM] Ysf Hamisu Sani: ME KE SHUGABANCI BA WA KE SHUGABANCI BA "To, ka ga akwai abubuwa guda biyu; akwai wane

SHIRU AKAN TA'ADDANCI JAMI'AN TSARO A SOKOTO YANUNA DA HADIN BAKINSU AKAYI.

Image
Yin Shirun Hukumomi Ga Ta'addancin Jami'an Tsaro A Sakkwato Ya Nuna Mana Da Haɗin Bakinsu Aka Yi –Sheikh Sidi Munir Sakkwato Mun ji mamaki matuƙa akan yin shiru da gwamnatin jahar Sakkwato haɗi da masarauta suka yi akan wannan ɗanyen aiki na jami'an tsaro da ya faru, wanda a matsayinsu na shuwagabanni al'umma to ya kamata a ce sun yi magana ko ba komai muma ƴan jahar Sakkwato ne ba daga wani guri muka zo ba, mun ji kuma mun gani a watannin baya da wasu Sojojin sama suka kufce suka buɗewa mutanen unguwar Mabera dake cikin garin Sakkwato wuta saboda an taɓa budurwarsu har suka kashe wata mata, gwamna ya yi Allah waddai da abin da ya faru har ya ce za a hukumta su waɗannan Sojojin. Amma mu a ɓangaren mu har ya zuwa Yau ɗinnan babu wani wanda ya buɗa baki ya yi magana akan wannan ta'addancin da jamin tsaro suka yi a kan mu, gwamna ko sarki ko wani Malami, haka kafafen yaɗa labarai. Wannan ne yake tabbatar mana da cewa wannan abin da ya faru da sanin gwamna ya faru

LABARI MAI MATUƘAR SOSA RAI

Image
Labari Mai Sosa Rai. DA MUN SAN BAKU DA MAKAMAI DA MUN KASHE KU TUN CIKIN DARE.       Inji Aliyu Adamu Tsoho Jos       --Idishia Jos. Wannan maganar ta fito ne daga bakin Sojojin Da Suka Zo Kisan 'yan'uwa Hussainiyyah Bakiyatullah. -Akwai wani dan uwa da na Ganshi yana salloli da addu'a a zaune tun zuwa na Hussainiyya har aka kammala wakiya bai tashi a wannan wajen ba. -Tun isowa na Hussainiyya Bakiyatullah ake budewa wuta akan 'Yan'uwa haka muka kwana ba su bari ba. -Munyi waya da Malam Turi a lokacin da nake cikin Hussainiyya yake tambaya na ina inane nace ina Zariya yace kun koma makaranta ne nace mai a Amma yanzu haka ina Hussainiyya sai yace to kace abin ya ritsa daku nace mai a. -To, bayan kallama Kammala Muzaharar Kano sai Malam Turi ya kara kira yake tambaya yanzu wani hali kuke ciki ? sai nace mai gasu nan sai harbi suke kuma mun samu labari sun wuce gyellesu a take yace muma gamu nan mun taho Zariya insha Allah. -Washe gari bayan Sallah As

43 Foreign Body Bullet Shrapnel Lodged in the Body of Sheikh Ibraheem Zakzaky

Image
43 Foreign Body Bullet Shrapnel Lodged in the  Body of Sheikh Ibraheem Zakzaky voiceofsheikh@gmail.com :A recent Radiology scan dated 22/10/2019 of the leader of the Islamic Movement in Nigeria, Sheikh Ibraheem Zakzaky, revealed that there are 43 Foreign Body Bullet Shrapnel that are presently lodged in his body as a result of the rain of bullets he was subjected to by the Nigerian army during the Saudi-sponsored # ZariaGenocide.As we can see from the accompanying photos his left eye was totally destroyed by the bullets of the Terrorist Nigerian army.Bullets Tips are made of lead. I knew this when I did my Industrial Attachment at the Defense Industries Corporation (DIC), Kaduna, in 1992. I was taught how to manufacture bullets. After gunshot what penetrate the human body is the lead portion of the bullet. This result to #Lead poisoning that contaminate the blood and poison the  body.The whole world is aware that Sheikh Zakzaky is in need of urgent medical attention but the gang

SAYYID ZAKZAKY (H) GA ALLAH YA DOGARA

Image
DOGARO GA ALLAH SHINE BABBAN MAKAMIN JAGORANMU Ina iya tunawa, ance a daren Waki'ar Zariya, lokacin da Sojojin Nigeria suka fara shela ga yan uwa da ke Husainiyyah akan su fito su mika wuya (Surrender) ba za a musu komai ba. Sun nemi Jin ta bakin Jagora, akan su fita ko su ki? Amsar Jagora, Sayyid Zakzaky garesu shine su dake su dogara ga Allah. Washe gari da safe, da wasu 'yan uwa masu Iklasi suka je suka roki Jagora Zakzaky (H) akan za a samar da hanyar da za a fitar da su, abin da Malam ya nuna shine ya fita ya je ina? Sauran wadanda aka kashe ba mutane bane? Su Malam suka ce; "Mu tsaya kawai mu dogara ga Allah." Ba ku ji audio din wayar da Shaikh Zakzaky (H) ya yi da wani Brother Husain ba a safiyar Waki'ar? A yayin da yake cewa Malam ya zai yi da rayuwarsa alhali tana cikin hadari? (Dama a lokacin Sojoji sun kashe mafi yawan yan uwa sun fara saka wuta a gidan Shaikh Zakzaky alhali yana cikin gidan), Amma abin da Malam Zakzaky yace masa shine; "Babu

WAN'NAN ZALUNCIN YA ISA HAKANAN

Image
LALLAI FA A SAKI SHAIKH ZAKZAKY! ZALUNCIN YA ISA!! A wata irin wannan wata na Disamba, 2015 gwamnatin Tarayyar kasar nan ta aiwatar da shirin da ta dade tana kullawa na yunkurin halaka Jagoran Harkar Musulunci, Shaikh Ibraheem Zakzaky da ma murkushe Harkar gaba daya. Sai dai ba kamar yadda suka so ba, Allah ya tseratar da rayuwar Jagoranmu, kuma Harkar ta ci gaba da wanzuwa. Amma duk da haka sun yi barnar da a tarihin kasar nan ba a taba yi wa wata jama’a irin ta ba, don kuwa sojojin Nijeriya sun kashe mutane sama da dubu guda. A cikin su akwai mata masu ciki da yara kanana. Sun kone tare da rushe gidan Jagoranmu da Cibiyar Musulunci ta Husainiyya Baqiyyatullah. Har ila yau tun bayan aukuwar wannan kisan kiyashin na Zariya, mun rika fitowa muna muzaharorin lumana don neman a bi mana hakkinmu, a yi adalci, a saki Jagoranmu da aka raunata da harbin bindiga, amma ba abin da aka rika tarbar mu da shi sai kisa, dauri da cin zarafi iri-iri. A irin haka gwamnatin Buhari ta kashe akalla mu

ANKAR RAMA JAGORA SAYYID IBRAHIM ZAKZAKY(H)

Image
An Karrama Jagora Sheikh Zakzaky (H) a Haramin Sayyida Ma'asuma (AS) dake Qom. Sayyida Suhaila ce ta amshi yautar bayan taron tunawa da shekaru 4 da Waqi'ar Zariya da aka gabatar a cikin Haramin Sayyida Ma'asuma a Birnin Qom Maitsarki.👇👇 https://youtu.be/gHZTPGyshZ0

TUNATARWA TARE DA AMMAR M.RAJAB

Image
ADDININ MUSULUNCI ADDINI NE NA KAMALA Daga Ammar M. Rajab Addnin Musulunci addini ne na kamalar mutum, kuma mafi girman tsarin kamala ita ce soyayya. Hakazalika soyayyarnan tana da tasiri mai girma wajen tabbatar da tsarin da Allah ya sanya a Musulunci domin ci gaban al'ummar Bani-Adama. Imam Muhammad Bakir ya siffanta Musulunci da cewa; ba komai bane fa ce soyayya da kaunar juna. Alkur'ani mai girma, littafin Allah ya siffanta Allah ta'ala ga mutane da cewa; shi mai tausayi ne, mai so da kauna, kuma mai son bayinsa. Tabbas wannan Ubangijin ne ya kafa turakun gini na shari'ar Musulunci wacce ita ce shari'ar dukkanin Annabawa a bisa asasin kaunar juna da soyayya. Har wala yau Allah ta'ala ya saka ka'ida na saka soyayya ga mutane a kan jagororin addini da sauran shugabannin siyasar tafiyar da al'amarin al'umma. Wannan yasa ya zama lazim jagorin addini da na siyasa su kira al'ummarsu zuwa ga kauna da soyayya a tsakaninsu da kuma kiransu zuwa

TAYA MURNAR ZAGAYOWAR RANAR HAIHUWAR YESU ALMASIHU( A.S)

Image
DAGA ZAUREN JAWABAN MALAMANMU. Amamadin Ma'aikatan wannan Zaure mai suna a sama "JAWABAN MALAMANMU", muna taya 'yan uwanmu a dan' Adamtaka da kuma kasancewa 'Kasa daya wato Kiristoci, Murnar zagayowan ranar Haihuwar daya daga cikin Manya-manyan Manzannin Allah a doron Kasa,Annabi Isa Almasihu(A.s),kamar yadda yake a Lissafin Shamsiyya. Mu(Musulmi) da ku (Kiristoci),mu yi amfani da wannan rana wajen fahimtar da junanmu muhimmancin dorewar zamantakewarmu akan zaman lafiya da ci gaban Kasa, da kuma wanzar da sada zumunci irin na Adamntaka a tsakaninmu.Mu kuma yi amfani da wannan damar wajen kara yin kiraye-kirayen wanzuwar zaman lafiya a tsakaninmu, duba da yadda Allah ya 'kaddara kasancewarmu A Kasa daya wadda ake kira Najeriya,ba mai korar wani. Da fatan za a yi shagulgulan Ranar Kirsimeti Lafiya a kare lafiya. Tsarki ya tabbata ga Mahaliccin sammai da Kassai,wanda ya fifita sashen Annabawa akan sashe.Allah ya kara girman Daraja da daukaka ga tsarka