Posts

Showing posts from February, 2020

Hana Bara Ko Almajiranci: Shaikh Yakubu Yahaya Katsina Ya Maganta Tare Da Ba da Mafita Akan Haka.

Image
A cikin wasu Jawaban Maulidai da shahararren Malamin Addinin Musuluncin nan kuma wakilin 'yan uwa musulmi Almajiran Ibraheem Alzakzaky da ke a Jihar Katsina,Shaikh Yakubu Yahaya ya yi a kwanakin baya a loacin da aka soma rufe wasu makarantun horo da gyara tarbiya a Katsina,Daura da Kano bisa zargin ana abubuwan assha a wadannan cibiyoyi,Malamin ya maganta tare da aike wa da sako mai dauke da samar da mafita ga hukumomi akan kokarinsu na dakile bara ko almajiranci a jihohi da ma kasa baki daya. Duk mabambantan Jawaban nasa,Malamin ya kuma bayyana ra'ayinsa da yadda yake kallon za a magance wannan matsala tsakanin 6angarorin biyu;hukuma da kuma su masu bara ko almajirancin Ga dai wani yanki na Jawaban nasa da muka gutsuro maku: “To abin da muke kallon wannan(rufe makarantun Allo) shi ne mukaddima na rufe makarantun Allon duk kasar nan baki daya.Domin yanzu abin da gwamnati ke 6a6atu akan shi shine makarantun allo sun dame su da bara;ba su son bara. Ba mu ce bara addini ne

DANGANE DA WATAN RAJAB

Image
*DANGANE DA WATAN RAJAB* *Daga Shaikh Ibraheem Zakzaky (H)* Rajab, idan mutum ya duba Mafatihul Jinan, a yayin da yake kawo ayyukan shekara ya fara da watan Rajab ne. Yana cewa; shi ne kamar watan farko a ayyuka.  Rajab, Sha’aban, Ramadan, watanni masu ayyuka na ibada. Saboda haka ya kamata mutum ya yi shirin shiga Rajab. Akwai ayyuka na musamman na daren farko na Rajab. Kar mutum ya yi sake. Daren farko da kuma, musamman azumin farkon Rajab din. Ya tashi da azumi daya ga watan Rajab. Da Rajab da Sha’aban da Ramadan, watanni ne masu darajar gaske. An samo hadisai daban-daban a kan falalolinsu. A cikin Ikbal A’amal, na ga shi Sayyid bn Dawus ya kawo wani dogon magana a kan cewa; ka sani dangane da falala an samo ruwayoyi da yawan gaske. To, ko da a ‘ka’idatul man balagah’. Idan ka san wata ka’ida ana ce ma ta ‘ka’idatul man balagah,’ hadisi ne aka samu daga A’imma daban- daban ma. An samu daga Imam Bakir da Imam Ja’afar da Ai’mma (AS) daban-daban cewa;

WAYASANI MA KO RASHIN GYARUWAR MU KE DAKATAR DA FITOWAR SU MALAM

Image
Waya Sani ma Ko Rashin Gyaruwar Mu Ke Dakatar Da Fitowam Su Mallam (H) Din? Eh, to! maganan Gaskiya, kowanne cikin mu yasan abinda ke aikatawa a boye a hasken rana ko cikin duhu. Yau da ace a tara dukkanin matasan wannan harkar wadanda suke Dass, Bauchi, Kano, Katsina Abuja da Sokoto dama Zariya da Kaduna dama dukkan sauran yankunan kasar nan, bansan yawan mu ba amma nasan lissafin Miliyoyi za'ayi kuma tabbas munkai haka. Ba ina magana yara bane, a'a matasa da suka mallaki hankalin su. Ace mana kowannen mu ya biya hakkin shuhada da ake binshi bashi na baya, wallahi da zamu biya, adadin kudin zai iya sayan babban mota da Jari dukkan iyayen Shahidan harkar nan duka! Kuma yabada dama a biya kudin makarantan 'ya'yan Shahidai su zama lauyoyi da Injiniyoyi da likitoti wallahi ba wasa nake ba. Amma meke faruwa? Bamu da kudin ne? A'a kawai bamu gama yarda gaskiya muke kai ba. Kuma bamu girmama maganan Jagoran harkar. Nasan akwai iyaye a cikin mu, ko kaine akace maka w

MALA'IKA JIBRILU SAIDA YA SHAWARA NB DA ANNABI LOKACIN DA ZAI FARA YIMASA WAHAYI. Ba maƙure shi yayi ba

Image
"Mala'ika Jibrilu sai da ya nemi Izinin manzon Allah ranar da ya fara kawo mashi sako,ba makure shi yayi ba" -Shaikh Yakubu Yahaya Katsina. Daga Auwal Isa Musa. A cikin Jawabin da Malamin Addinin Musuluncin nan a 6angaren 'yan uwa Musulmi almajiran Shaikh Ibraheem Yaqoub Alzakzaky na Katsina, Shaikh Yakubu Yahaya ya gabatar a ranar Lahadin nan na tunawa da ranar Yaumul-mub'ath wato ranar da aka fara aiko manzon Allah(S) da Sako zuwa ga Talikai,Malamin yace; Mala'ika Jibrilu(A.s) bai ta6a razana manzon Allah(S) balle makureshi ko kuma wahalar da shi ba tun da yake zuwa kawo masa sako,bilhasali ma yana neman izininsa ne a duk lokacin da yazo garesa. Malamin ya kara da cewa; a lokacin da Manzon Allah ya kai shekara Arba'in. sai Allah ya turo mala'ika Jibrilu da sakon Annabta da Ayar nan ta 'Ikra'a,amma da yazo ya sami Manzon Allah a kogon Hira sai da ya nemi izin shiga wajensa,ba matse shi yayi ba:  "Wata ruwayar a falke (Jibrilu) ya

NIFA ABINDA ZANCE SAIDAI AYI HAƘURI DANI- Bilya Hamza Dass

Image
Angama Maganan Kotu Ko? To Ni Ga Abinda Zance, Sai Dai Ayi Hakuri Dani. Abokin ku, Bilya Hamza Dass Nagama ganin 'yan uwa sunyi ta kawo rahotannin abinda yafaru a kotu yau harda zuwa hutu da kuma dawowa da yanda aka kare har bada doka ta biyu da Alkali ya bayar na cewa lalle abaiwa likitotin su Mallam daman ganin su ko yaushe. Tare da maganan sake sanya watarana da akace kamar 23 da 24 na watan 4 domin cigaba da zaman! Toh! Allah yafada a littafin shi me tsarki cewa; baze taba daura kafirai akan masu imani ba. Wani wajan yace; 'Hakki ne akan mu mu temaki masu imani' (Aya). To gashi munyi imani kuma har mun zamu “Victims” na imanin mu ga Allah ta'ala kuma gashi azzalumai nata kadamu da cutarwa menene ke faruwa? Karka raba 1 zuwa 2, magana ta Allah bamu shirya tsakanin mu da Allah bane. Ranar wanka be kamata ayita boye ciki ba, domin shima yana bukatan a wanke shi. A baya muna hangen munanan ayyuka daga wajen mu muna bada misalai dasu muna gujewa tare da addu'

TARON MATASA KARO NA 27 A GARIN BAUCHI- Nasihohin Sheikh yaqub yahya katsian.

Image
Taron Matasa Karo Na 27 A Garin Bauchi: Rahoto Na Biyu: Nasihohin Sheikh Yakubu Yahaya Ga Matasa Daga Bilya Hamza Dass “Ba sai anzo wajan taro (Mu'utamar) kafin a dinga tashi ana sallar dare ba, wannan wani abu ne muhimmi, hasalima yana daga cikin manyan alamomi da ake gane mumuni” inji shi. A wani bangare na jawabin nashi babban bako me jawabi a wajan Sheik Yakubu Yahaya yaja hankalin matasa wajan kula da Ibada musamman a shekarun su na matasan taka. Yace “Abinda su Mallam suke so shine su samar da wasu mutane wadan da Allah zai damka musu amanar al'umma, wadanda zasuce Allah yayi kuma yayin” kuma wannan alkawari na shi. Yakawo misalai yanda Allah yake zabar wasu dai-daikun bayin shi ya damka musu amanar al'umma, yayin da yaga tsaran su greshi da kuma amanar su. Misali Imam Kumai ni (R) da Shehu 'Dan Fodiyo wadanda wadanan sun faru shekaru kadan baya. Yace to wannn shine hankoron su Mallam (H) yace ya bayyana ba sau daya ba, cewa babbn gudumawa da wani zai baya

KWANAKIN DA AKA SHIGA KOTUN SU SHEIKH ZAKZAKY A TSAWON SHEKARA BIYU

Image
KWANAKIN DA AKA SHIGA SHARI'AR SHAIKH ZAKZAKY A TSAWON SHEKARU BIYU 1— 15/5/2018 2— 21/6/2018 3— 2/8/2018 4— 4/10/2018 5— 7/11/2018 6— 22/1/2019 7— 25/3/2019 8— 18/7/2019 9— 29/7/2019 10- 5/8/2019 11- 5/12/2019 12- 6/2/2020 An shiga shari'ar sau 12, kuma an je da su Shaikh Zakzaky da mai dakinsa kotun sau kusan 5, a yayin da zama 7 ba su halarta ba, saboda yanayoyin jikinsu. Ko da yake so daya ba a yi zaman kotun ba, a ranar da aka ce Keke Napep ya mangare Alkalin. Duk wadannan kwanaki 12 din a tsawon shekara biyu har yanzu ba a fara gabatar da shari'ar ba. Kamar yadda ma kowa ya sani, sai gobe Litini da Talata ne za a cigaba da shari'ar, inda wai ake sa ran za a karantowa su Shaikh Zakzaky tuhumar da ake musu su amsa ko su kore shi. Kafin a fara shari'a. Tabbas tarihi zai rubuta ya kuma taskace duk wani nau'in zalunci da azzaluman mahukuntan Kasar nen ke yi wa Shaikh Ibraheem Zakzaky da almajiransa, ba abin da za a manta ko a bar shi ya bace,

MUN SAKE KADA GWAMNATIN KADUNA A KOTU

Image
Takardar Sanarwar Manema Labarai: MUN SAKE KA DA GWAMNATIN JIHAR KADUNA  A KOTU Harkar Musulunci a Nijeriya a ranar Juma’a, 21/2/2020 ta kara samun nasara a hukuncin da babbar kotun jihar Kaduna ta yanke a kan karar da aka shigar na sauran ‘yan’uwa Musulmi da ake tsare da su tun cikin watan Disambar shekarar 2015 biyo bayan mummunan harin da Sojojin tarayyar Nijeriya suka kaddamar a Zariya. Kotun ta wanke tare da sallamar dukkanin wadanda ake zargi su kusan dari, abin da ke tsame Jagoran Harkar Musulunci a Nijeriya da ma mabiyansa daga aikata duk wani laifi na lamarin da ya kai ga kisan kiyashin Zariya. Wannan yanke hukunci ya kawo karshen shari’ar da aka kwashe shekaru hudu cur ana kwafsawa, inda gwamnatin Jihar Kaduna ta yi karar kimanin ‘yan uwa Musulmi na Harkar Musulunci kusan dari biyu bayan harin da Sojojin Nijeriya suka yi a cikin watan Disambar 2015, wanda ya sabbaba kashe rayukan fararen hula sama da dubu daya wadanda ba su aikata laifin komai ba, tare kuma da yi wa gaw

Labaran Kanzon-Kurege: Malamin Addini Ya Gargadi Masu Rubuta Labarun Karya A Kafafen Sadarwa.

Image
An tsoratar akan rubuta labarun kanzon-kurege a kafafen sada zumunta na zamani. Daga Auwal Isa Musa. An tsoratar da kuma yin gargadi dangane da rubutawa tare da yada labaran karya da suka zama ruwan dare a kafafen sada zumunta na zamani(social media). Malamin addini a 6angaren 'yan uwa musulmi a Katsina,Shaikh Yakubu Yahaya Katsina ne ya yi wannan jan hankalin a lokacin da yake gabatar da lakca a wani taron karawa juna sani na kwanki biyu akan 'hanyoyin da za a kaucewa yada labarun kanzon-kurege da yadda za a cin moriyar kafafen sada zumunta na zamani' wanda 'yan uwa musulmi almajiran shaikh Ibraheem Alzakzaky suka shirya a karshen makon nan da ya gabata a Katsina. Malamin ya bayyana cewa,lallai a guji rubutawa da yada labarun karya wadanda ba su da makama balle tushe a cikin wadannan kafafe duba da yadda hakan ke tasiri ga al'umma cikin dan karamin lokaci,wanda su kan haifar da hargitsi da tada fitina da dasa kiyayya a tsakanin juna,inda yace "Kar ya z

Kotu Ta Yi Wa Wani Matashi Hukunci Sakamakon Batanci Ga Shaikh Zakzaky.

Image
Wata Kotu ta daure wani Matashin akan ya yi 6atanci da Hoton Shaikh Alzakzaky. A ranar talatar na da ta gabata (4/2/2020) ne, wata Kotun Majistare da ke Potiskum jihar Yobe ta yanke wa wani matashi mai suna Mohamad Garba hukuncin daurin watanni shida a gidan kaso ko kuma tarar Naira dubu 10,000 a bisa samunsa da laifin 6ata sunan Malamin Addinin Musulunci shugaban 'yan uwa Musulmi a Najeriya, Shaikh Alzakzaky,ta hanyar amfani da Hoton Malamin a cikin wani bidiyon 6atanci da ya yi wa wasu Mata ya sakie shi a kafafen sadarwa. Bidiyon mai tsawon mintuna biyu da dakika 40 da Matashin ya saki kafafen sadarwa na zamani a ranar 26 ga Janairun 2020,ya nuna yadda yake 6atanci ga wasu matan da ba su da Hijabi a jikinsu yana kuma tallatasu da cewa "ana gwanjonsu",a inda daga karshen bidiyon ya dauka da Hoton Malam Alzakzaky, sakamakn haka Almajiran Malamin suka yi kararsa da sunan ya yi 6atanci da zub da Mutunci wa Malamin nasu. Almajiran Malamin sun binciko matashin sukakuma

Kotun Tarayya A Kaduna Ta Ba Da Odar Barin Likitocin Shaikh Zakzaky Su Rika Ganawa Da Shi A Gidan Yarin Kaduna.

Image
SHARI'AR SHEIKH ALZAKZAKY: Kotun Tarayya da ke Kaduna a zamanta na yau Alhamis domin ci gaba da sauraren Karar da gwamnatin Jahar ta shigar akan wasu tuhumce-tuhumce da ta ke yi wa Jagoran 'yan uwa Musulmi Shaikh Ibraheem Alzakzaky da mai dakinsa Malama Zeenatu,Kotun ta ba da umurnin a rika barin Likitocin Shehin Malamin su rika duba lafiyar sa a cikin gidan Yari a duk lokacin da suka bukaci haka. Shehin Malamin dai na ci gaba da tsarewa ne tun Watan Disambar 2015,biyo bayan kashe daruruwan Almajiransa, 'yayansa da wasu 'yan uwansa na jini a yayin da shi kansa da Matarsa ba su tsira daga halbin harsasan da Sojoji suka yi masu wanda har yau suke cikin rashin lafiya sakamakon illar da harsasan su kai masu a jiki. Za dai a ci gaba da sauraren karar ne a ranar 24 da 25 na watan da muke ciki,bayan rashin halartar Malamin da Matarsa a zaman Kotun na yau sakamakon rashin lafiyar da ke su fama da ita, kamar yadda Lauyan Malamin Femi Falana ya bayyana. Menene ra'ayinku

SABON MAKIRCIN EL'RUFA'I GA SHEIKH ZAKZAKY

Image
Shari’ar ‘Yan’uwa A Kaduna: Sabon Makircin El-Rufai Ga Shaikh Zakzaky Daga Ammar M. Rajab Idan ba ku manta ba gwamnatin Kaduna a karkashin gwamna Nasir El-Rufai ta gurfanar da ‘yan’uwa Musulmi almajiran Shaikh Zakzaky kusan 200 a kotun Kadunan tun bayan kisan kiyashin da sojojin Nijeriya suka yi a kan ‘yan’uwa a ranekun 12-14 ga watan Disamban 2015. Da yammacin ranar Talatar 31 ga watan Yulin 2018, Alkali D.S. Wyom ya kori karar da gwamnatin Kaduna take yiwa ‘yan’uwa Musulmi almajiran Shaikh Zakzaky kusan 100 inda ta wanke su tare da sakin su. Dama shari’ar ta ‘yan’uwa an raba ta gida biyu ne, inda tun bayan wannan sakin, aka ci gaba da shari’ar dayan bangaren. Wanda ya zuwa hada rahoton nan tuni aka kammala karbar duk wata shaida, inda Alkaliya yanke hukunci kawai ake jira daga gare ta. Sai dai wata majiya mai tushe ta tabbatar mana da cewa; hukuncin wanda Alkaliyar ta kasa yanke wa a zama biyu hakan ya faru ne sakamakon barazanar da gwamnan Kaduna yake yi mata. Rahotannin s