Posts

Showing posts from January, 2020

HALIN DA ƘASA TAKE CIKI. ANRUFEWA SARAKUNA BAKI NE- Sultan Sa'ad Abubakar.

Image
Halin da kasa ke ciki A Najeiya: ' An rufewa Sarakuna da Malaman Addini baki ' – Sarkin Musulmi Mai alfarma Sarkin Musulmi kuma Shugaban Majalisar Koli ta Harkokin Addinin Musulunci, Alhaji Muhammadu Sa’ad Abubakar, ya ce sarakuna da malaman addini da ya kamata su rika sanya ido kan shugabannin siyasa wajen suna yin abin da ya dace, an rufe musu baki. Sarkin Musulmi ya bayyana haka ne lokacin da yake jawabi a wajen taron Tattaunawa a Tsakanin Addinai kan Zaman Lafiya karo na Uku na bana da aka gudanar a Abuja. Taron ma taken “Tattaunawa a Tsakanin Addinai: Karfafa Al’adar Zaman Lafiya da Adalci da Sulhuntawa, Mai martaba Sarkin Kano, Malam Muhammadu Sanusi II, ya wakilce shi a taron. Ya ce: “Duk wanda ya kashe wani Kirista ko Musulmi mai aikata babban laifi ne kuma a haka ya kamata a dauke shi. Duk abin da nake ji a yau mamaya ce. Sarakuna da shugabannin addini da ya kamata su  sanya ido kan shugabannin siyasa don su aikata daidai ga jama’a,  an tilasta su yin shiru. Id

SALLACEWAR SOYAYYA BAYAN AURE.da yanda za a magance ta.

Image
*An bayyana Sallacewar dandanon Soyayya bayan Aure da rashin aza tubalinta tun farko saboda Allah.* Daga *_Auwal Isa Musa._* Malama Hadiza Wowo ta bayyana haka a lokacin da take gabatar da Lakca ga Ma'aurata,a wata Walimar Aure a ranar Alhamis din nan a Katsina. Malamar ta ce,zamantakewar auren nan da ake yi tana da Ka'idoji da Sharudda da Allah ya gindaya kuma muke da abubuwan koyi a zamantakewar daga Fiyayyen Halitta Manzon tsira(S) wanda shi ne makura a wajen kowace irin kyakkyawar dabi'a,wadda har Allah ya lazimta mana koyi da shi a cikin dabi'un,amma abin takaici yau an wayi gari masu shirin yin Aure har ma da yawa daga wadanda suka yi auren, ba su da masaniyar wadannan ka'idoji ko kuma sun yi watsi da su suna aikata son zuciyarsu. A wani bangare na jawabinta,Malamar,ta kuma Kalubalanci Masoyan da Soyayyarsu.                                                    ke disashewa nan-da-nan kafin aje ko'ina bayan Aure,inda ta kwatanta hakan da rashin aza tu

HALIN DA IS'RAILA DA YAHUDAWA SUKE CIKI TUN BAYAN HARIN SOJIN IRAN A SANSANIN AMURIKA A IRAQ

Image
Nasir Isa Ali. -Halin da Israila da Yahudawa ke ciki tun bayan kashe Janar Qassim Sulaimani. -- Rahotanni sun tabbatar da cewar,manyan jami'an gwamnatin Isaraila sun shiga wasan buya,tare da yin kaffa-Kaffa wajen yin tafiye tafiye da yawan bayyana wajen taro tun bayan harin da Iran ta kai kan sansanonin sojan Amurka dake cikin kasar Iraqi. Domin hakan ya nuna cewar,Iran din zata hararsu a ko'ina cikin yankin Asiya. Daya daga cikin hujjojin dake tabbatar da hakan shine, kafin kai harin na Iran kan Amurka,an shirya cewar Ministan harkokin kasashen waje na H.K.Israila, Mr.Yisrael Katz zai ziyarci birnin Dubai dake UAE domin halartar wani taron baje koli a tsakiyar wannan watan na Junairu,amma sai aka janye ziyarar,kuma babu wani dalili kan janyewar. Amma jami'an ma'aikatar tasa ta harkokin waje sun sanar da cewar,an yi hakan ne bisa wasu manyan dalilai na tsaro. - Tun dai bayyanar wani rahoton sirri dake nuna cewar,shugaba Trump yayi amfani ne da wani rahoton sirri

AL'ƘALAMI KAFI REZA KAIFI. TARE DA M.I GAMAWA-Janar ƙasim suleimani: Amurika ta hadiyi tabarya.

Image
*ALKALMI KA FI REZA KAIFI* TARE DA M. I. GAMAWA *Janar Qaseem Soleimani: Amurka ta hadiyi ta barya!* Wata mas'ala da marubuci ke fama da ita a kullum, musamman rubutu a kan abin da ke gudana a yau da kullum shi ne rashin tabbas kan abin da zai rubuta. Fakam da yawa mai rubutu na iya kimtsawa tsaf don rubutu a kan wani abu, amma sai sawun giwa ya taka kafar rakumi. Na shirya don maida wa wani kumurcin Farfesa da ke amsa sunan Malamin tarihi a Nijar martani kan jahilcin da ya nuna game da tarihin Shehu  Dan Fodiyo, Hasken zamani, amma sai sawun giwa ya take na rakumi. Mun taka birki don magana a kan Qaseem Soleimani, wanda Amurka ta kashe a satin da ya gabata. Soleimani ya tafi kasar Irak a matsayin dan sakon kasarsa Iran bisa gayyatar da ita kanta kasar Irak ta yi masa. Ashe tafiyar ita ce ta karshe. Abin da ya samu wannan gwarzo shi ne abin da yake nema tuntuntuni. Abin nema ita ce SHAHADA. Yanzu Allah ya yi wa Janar Sulaimani gyadar dogo da abin da ya fi so fiye da k

FACEBOOK YACE ZAI ƘULLE DUK WANI ACCOUNT DA YA ƘARA YIN RAFOTO AKAN GEN QASIM SULEIMANI

Image
Facebook Ya Haramta Saka Duk Wani Abu Da Ya Shafi Kasim Sulaimani Muma Abinda yasa bamu sanya fotonsa ba don kada su share. Janairu 12, 2020 - 1:05 PM Kamfanin sadrwa na facebook ya bada sanarwan daga yanzu zai rika cire duk wasu abubuwa da aka dora a kan shafinta danganci Kasim Sulaimni. Taskar watsa labarai ta Ahlul-Baiti-ABNA24- ta rawaito a cikin wata sanarwa da kamfanin facebook ya fitar a jiya, ya ce daga yanzu zai rika cire duk wani abu da aka dora a kan shafinta ya shafin Janar shaheed kwamandan sojojin Iran da Amurka ta kashe mako goda day a gabata da kuma duk wani abu da ya shafi dakarun kare juyin juya hali na kasar Iran. Bayanin ya ce kamfanin zai yi aiki 100% da dokar ta kasar Amurka wacce ta haramta duk wasu aikace-aikace da suka shafi dakarun kare juyin juya hali a kasar Iran, kuma zai share duk wani shafi da aka saka wani abu makamancin hakan. Tun daga lokacinda Amurka ta kashe shaheed sulaimani a makon da ya gabata ya zuwa yanzu, facebook ya share shafuffuka n

KUKALLI JAWABIN C.I.A DAGA AMERIKA KUJI GASKIYAN DALIN DAYA YASA SUKA KA...

Image

EL-RUFA'I ƊAN TA'ADDA NE.

Image
WATA SABUWA: 'Elrufa'i kai ne ka yi wa Mutanen Jihar Kaduna Laifi,ba Shaikh Zakzaky ba' -Mabiya Alzakzaky. "A tsawon shekaru 40 cur na da'awarsa, Shaikh Ibraheem Zakzaky bai ta6a afkawa wani ba, kai ko cin bashin wani ya ki biya bai ta6a yi ba! Wani bai ta6a kai shi kara wajen yan sanda akan ya cuce shi ko ya take hakkinsa ba. Magoya bayansa ba su taba kwashe kayan wani ko su zubar masa a yayin taron su ba, bare su je su dira kan wani ko su kashe shi. Ba a taba yi ba! Kai kuwa Elrufa'i, sakataren gwamnatinka, ya fada karara cewa bayan da sojoji suka dira a kan Shaikh Ibraheem Zakzaky, inda suka kai kansu gidansa cikin dare, suka rika bude wuta, suka kwana biyu suna harbin almajiransa har sai da suka kashe daruruwan al'ummar Nijeriya, kai ne ka ba da umurni tare da wakilta wasu daga gwamnatinka, suka je suka taya sojoji haqin rami tare da bizne bayin Allah, al'ummar Nijeriya, mafi yawa 'yan jihar Kaduna, kuma Musulmi, su kimanin 347 a ramin bai-d

HABA DAKTAN MAƘARYATA KO ƊAN FIRAMARE ASIYASA YASAN WACE ƘASACE TAKEDA ALAƘA TA ƘUD'DA ƘUD DA AMERIKA.

Image
Yanzu ka ce da Sani Rijiyar Lemo ya nuna a ina Iran ta ke a taswirar duniya to sai dai ka kwace limancinsa indai ba ka hada masa da sunan kasar a kan taswirar ba. Amma duk wata siyasar kasar sai ya shiga rediyo yana bayaninta. Ka ji tsoron Allah dakta. Duk abin da fa kake fada mala’iku suna nan suna rubutawa. Kada ka ga wai don kasar yan Shi’a ce sai ka yi ta karya kana zaton ba komai. Irinku ne fa suka gaya mana wai yan Shi’a sun ce Jibrilu manta sako ya yi ya bawa Annabi Muhammad ba Aliyu bn Abi Talib ba, muka duba muka ga karya ne. Kuka ce mana yan Shi’a suna da nasu Quranin, muka shiga nema a kasuwa aka dinga yi mana dariya! Ko dan firamare a siyasar duniya ya san cewa Saudi Arabia ita take da alaka ta kusa da Amerika. Kuma tun da aka yi juyin-juya-hali a Iran aka kifar da gwamnatin Shah ba a kara samun daidaito tsakanin Amerika da Iran ba. Amma wai an ce kai ka yi karatun nuna cewa bakin Amerika da Iran daya! Kai sai ka ce Amerika ba tare da Saudi Arabia suka hada kai wajen ya

EL-RUFA'I KUNTUGURMIN MAI LAIFI NE GA AL'UMAR JIHAR KADUNA

Image
Elrufa'i! KAI NE KAIWA MUTANEN JIHAR KADUNA LAIFI, BA SHAIKH ZAKZAKY BA! A tsawon shekaru 40 cur na da'awarsa, Shaikh Ibraheem Zakzaky bai taba afkawa wani ba, kai ko cin bashin wani ya ki biya bai taba yi ba! Wani bai taba kai shi kara wajen yan sanda akan ya cuce shi ko ya take hakkinsa ba. Magoya bayansa ba su taba kwashe kayan wani ko su zubar masa a yayin taron su ba, bare su je su dira kan wani ko su kashe shi. Ba a taba yi ba! Kai kuwa Elrufa'i, sakataren gwamnatinka, ya fada karara cewa bayan da sojoji suka dira a kan Shaikh Ibraheem Zakzaky, inda suka kai kansu gidansa cikin dare, suka rika bude wuta, suka kwana biyu suna harbin almajiransa har sai da suka kashe daruruwan al'ummar Nijeriya, kai ne ka ba da umurni tare da wakilta wasu daga gwamnatinka, suka je suka taya sojoji haqin rami tare da bizne bayin Allah, al'ummar Nijeriya, mafi yawa 'yan jihar Kaduna, kuma Musulmi, su kimanin 347 a ramin bai-daya. Na farko bai buyawa duniya cewa da umurni

DAKARUN IRGC SUNYI KARIN BAYANI KAN RABO JIRGIN FASINJAN UKRAINE

Image
Dakarun IRGC Sun Yi Karin Bayani Kan Harbo Jirgin Fasinjar Ukraine A Iran шаблоны сайтов joomla Details   Published Date Written By Muhd Awwal Bauchi Category:  Latest Hits: 45 Kwamandan rundunar kare sararin samaniyyar ƙasar Iran na dakarun kare juyin juya halin Musulunci na Iran (IRGC), Birgediya Janar Amir Ali Hajizadeh yayi karin haske dangane da harbo jirgin  saman fasinjar ƙasar Ukraine da aka yi a birnin Tehran, babban birnin ƙasar ta Iran yana mai cewa haka ya biyo bayan kuskuren da aka samu ne, kamar yadda kuma ya ce babu wani ganganci cikin haka kuma babu wani ƙoƙarin ɓoye-ɓoye cikin jinkirin da aka samu wajen sanar da hakan kamar yadda wasu suke ƙoƙarin nunawa yana mai cewa wajibi ne a gudanar da ayyukan bincike kafin a sanar da haƙiƙanin abin da ya faru. Birgediya Janar Hajizadeh ya bayyana hakan ne a wata ganawa da yayi da manema labarai don ƙarin haske dangane da haƙiƙanin abin da ya farun inda ya ce: Ya samu labarin abin da ya faru na harbo jir

HARBO JIRGIN UKRANE BISA KUSKURE. Nashirya daukar duk wani hukunci da yadace dani- Birgedi janaral Ali Hajizadeh.

Image
---- Nasir Isa Ali Na shirya karbar duk wani hukunci daga hukumomi kan harbe jirgin kasar Ukiren (Ukraine) bisa kuskure. ---Birgediya Janar Ali Hajizadeh--- --- Babban kwamandar rundunar IRGC dake kula da tsaron sararin samaniyar kasar Iran,Birgediya Janaral Ali Hajizadeh ya bayyana cewar 'rundunarsa da aka kintsasu domin jiran ko-ta-kwana ne suka habo jirgin dakon farar hula na kasar Ukiren bisa kuskure a birnin Tehran. Ya kara da cewar,babu rufa rufa a wannan lamarin,kamar yadda wasu ke fada,kawai an yi kokarin tabbatar da hakikanin abin da ya faru ne,kafin kuma a sanar wa duniya da mutane Iran sahihin labarin jirgin. Yace lokacin da lamarin ya faru,shi yana can kudancin Iran yana kokarin kai hari kan Amurka,sai daga baya aka sanar da shi cewar,an harbo wani jirgi kusa da masaukin jiragen sama na Imam Khumaini dake Tehran. Yace ranar 8 ga wata ina kudancin Iran ne muna niyar kai wa Amurka hari,kuma mun kintsa rundunarmu a ko'ina cikin kasar da makamin kakkabo jirgin ya

HADARIN JIRGIN SAMAN ƘASAR UKRAIN KWAMANDAN DAKARUN KARE SARARIN SAMANIYAR IRAN YAYI ƘARIN HASKE.

Image
Tabbas harbo jirgin fasinjar Ukraine da ya faru a Tehran bisa kuskuren dakarun kasar wani abin bakin ciki ne da ke bukatar jami'ai su yi dubi cikinsa don guje wa sake faruwar hakan. Sai dai a daidai lokacin da mu ke taya iyalan wadanda lamarin ya ritsa da su juyayin wannan rashi su kuma wadanda suka rasa rayukansu Allah Ya jikansa, har ila yau kuma jami'an kasar Iran sun cancanci jinjinawa saboda yadda suka fito suka yi bayani da kuma daukar nauyin abin da ya faru wanda bisa kuskure ne hakan ta faru. Shi kansa wannan jaruntaka ce babba da kuma girmama al'ummominsu. Zuwa an jima da yardar Allah zan kawo maka karin bayani kan hakikanin abin da ya faru din ta bakin kwamandan dakarun kare sararin samaniya na Iran din, Birgediya Janar Amir Ali Hajizadeh.

KALAMAN AISHA DIKKO: Wasu 'yan uwa sun ja kunne gami da nasiha.

Image
KALAMAN A'ISHA DIKKO: Wasu ba'alin 'Yan uwa Musulmi Almajiran Shaikh Zakzaky sun yi gargadi tare da Nasihantar Kwamishiniyar Shari'a ta Kaduna,Aisha Dikko. Ga abin da suke cewa kamar haka: "A'isha Dikko! Ya kamata ki shiga taitayinki sosai akan al'amarin Jagoranmu Shaikh Ibraheem Zakzaky (H). Kila ke kina da Uba, kina da miji ma kila, kila kuma kina da 'ya'ya, kuma kina da rai kina son ranki, kina bukatar ki cigaba da cin duniya ko? Kila kina da dan ragowar mutumci a idon wanda suke ganin irinku da mutunci kuma." Sun ci gaba da cewa: "Muna miki nasiha kan ki yi kokarin ganin baki biyewa su Elrufa'i akan zaluncin da suke wa Shaikh Zakzaky ba. Kar ki yarda ki saka kanki a cikin Baqin Littafin makasan mutum fiye da 1,000 da Sojojin Nijeriya suka kashe a Zariya a shekarar 2015. Ki yi kokarin ganin baki nuna hannunki a cikin umurnin Elrufa'i na bizne daruruwan gawarwakin yan uwammu Musulmi a ramin bai daya a garin Mando ba

ZAMU HADA KAI DA IRAN DOMIN MUYAƘI AMURIKA-Banizuwala

Image
Zamu hada kai da Iran wajen yakar Amurka (Banizuwala) - Kasar banizuwala (Venezuela) ta nuna goyon bayanta ga kasar Iran. ---Ministan tsaron kasar Banizuwala Gen. Vladimir Padrino Lopez ya tsine wa kasar Amurka bisa ta'addancin kashe shugaban masu yaki da yan ta'addan duniya,Laftana Janar Qassem Sulaimani,sannan ya yabawa Iran bisa kakkausar matakin martanin da ta dauka kan Amurkan. Janar Lopez ya bayyana harin da Amurka ta kai wa Janar Sulaimani da cewar'ta'addanci ne tsaba. -  Janar Lopez ya bayya wa ministan tsaron Iran,Janar Hatami ta wayar tarho cewar, da shi da mutanen Banizuwala suna mika jajensu tare da goyon bayansu ga kasar Iran,sannan suna yin Allah wadarai da Amurka da ta'addancinta. Ya bayyana harin da Amurka ta kai wa Janar Sulaimani da cewar,zafi Amurkan taji na cewar Sulaimani ya kawo karshen yaranta yan ISIS,don haka bari ta daukar musu fansa. Janar Padrino Lopez ya bayyana Janar Qassem Sulaimani da cewar 'mutumin kirki ne jarimin mara ts

KOTUN ICC TAFARA BINCIKEN KISAN KIYASHIN DA SOJOJI SUKAYI A ZARIA

Image
Daga Ammar M. Rajab Kotun hukunta manyan laifuffuka ta duniya (ICC) ta bayyana cewa ta fadada bincikenta dangane da laifukan yaki da take hakkin bil’adama a Nijeriya wanda rundunar sojojin Nijeriya suka aikata akan mabiya Harkar Musulunci a Nijeriya. Har wala yau kotun ICC din ta ce binciken na ta zai kuma shafi kisan da sojojin Nijeriya suka yiwa mabiya kungiyar masu rajin kafa kasar Biyafara wato IPOB. ICC din sun bayyana hakan ne a rahoton taron su na shekarar 2019 dangane da ayyukansu wanda ofishin bincike na kotun duniyar wanda Fatou Bensouda ke jagoranta. Rahoton wanda aka sanya masa kwanan watan 5 ga watan Disamban 2019, ya nuna cewa tun a ranar 18 ga watan Nuwamban 2010 aka kaddamar da fara binciken abubuwan da suka faru a Nijeriya. Har wala yau rahoton ya nuna cewa; ofishin bincike na ICC din, a ranar 12 ga watan Nuwamban 2015 ya gano; “Laifuka takwas na yaki da take hakkin bil’adama a karkashin makala ta 7 da 8 na ‘Roman Statutes.” Haka zalika duk a rahoto

SHAWARA GA 'YAN MATA- Sheikh Yaqub Yahya katsina

Image
SHAWARA GA 'YANMATA: '...Yan Mata Su Nisanci Karbar Kudi A Hannun Samari' - Shaikh Yakubu Yahaya. Daga Auwal Isa Musa. A wata 'yar gajeruwar shawara da ya ba Matasa Mata da yazo a kan wata ga6a a cikin karatun Tarbiyya da yake gabatarwa Matasa 'yan Uwa Musulmi Almajiran Shaikh Ibraheem Zakzaky na Mako-Mako a gidansa da ke Katsina,duba da yadda ake samun gur6atar Tarbiyya da kuma Mu'amala Marar kyau tsakanin Samari da 'yan Mata a wannan Shu'umin Zamani, Shaikh Yakubu Yahaya Katsina, ya an karar da 'yan Mata wani abu da ba su dauke shi bakin komai ba amma shi ne d'an Ba da ke kai su ga fadawa tarkon Shaidan da shaidanun Samari. A lokacin da yake an karar da su wannan Matsalar,Shaikh Yakubu Yahaya yace, ita Mace tana da wani abu a rayuwar; wanda ke ba ta shi ne nata. Ya ci gaba cewa,shiyasa idan ka cire Mahaifin Mace,ko yayanta,ko 'Kanenta,ko Kane da Wan Uba,ko Kane da Wan Uwa da sauran Muharramanta,to, ba a yarda Saurayi ya dauki Kudi y

KWAMANDAN DAKARUN IRGC YAYI IƘIRARI BAYANI DANGANE DA HARIN DA DAKARUN NASA SUKA KAI.

Image
Kwamandan dakarun kare sararin samaniyya na dakarun kare juyin juya halin Musulunci na ƙasar Iran, Birgeidya Janar Amir Ali Hajizadeh yayi ƙarin bayani dangane da harin da dakarun nasa suka kai sansanin sojin saman Amurka na Ain al-Asad da ke lardin Anbar na ƙasar Iraƙi inda ya tabbatar da cewa adadi mai yawa na sojojin Amurka sun halaka wasu kuma sun sami raunuka. Birgediya janar Hajjizadeh ya bayyana hakan ne a wata ganawa da yayi da manema labarai a yau ɗin nan Alhamis inda yayin da yake ƙarin bayani dangane da harin ɗaukar fansar jinin shahid Janar Ƙasim Sulaimani ya bayyana cewar: Wannan hari da makamai masu linzami kan ɗaya daga cikin mafi muhimmancin sansanin sojin Amurka yayin wannan harin, mafari ne na wasu hare-hare masu girman gaske da za su haɗe dukkanin yankin nan, kuma hakan wani lamari ne da wajibi ne a yi shi. Yayin da yake magana dangane da hasarar da Amurka ta yi yayin wannan harin da kuma kore ikirarin shugaban Amurka na cewa babu wani sojan Amurka da ya halaka

HAƘURI DA HANKALI DA IRAN TA NUNA SHINE BABBAN MATAKIN NASARAR FARKO GA MUMINI- Nasir Isa Ali

Image
Nasir Isa Ali. Hakuri da Hankalin da Iran ta nuna, babban matakin nasarar farko ga muminai. -------------- Da dama daga mutane (har da wasu yan Shi'a) sun zaci cewar,daga ranar da Amurka ta halaka Janar Qassem Sulaimani Iran zata fara kai hare hare kan Amurkawa da kadarorinsu domin yin ramuwar kisan Janar Sulaimani din. Amurka ta halaka Janar din ne a ranar Juma'a 3/1/2020 da misalin karfe 2 na daren juma'a a kan hanyarsa ta zuwa filin jirgin saman Bagadaza (Baghdad) tare da wasu muhimman mutane ciki har da mataimakin kwamnadan PMU Abul Mahdi Almuhandis da kuma mijin 'Yer shi Janar Sulaimani din. - Akwai Wani abokina wanda ya bugo min waya tun daga kasar Kanada yake tambayata cewar "shin Iran ta fara kai harin ramuwarta kan Amurka ne? Sai nace masa a'a. Sai yace min wai yaga wasu labarai suna yawo wai ana luguden wuta a barikokin Amurka da sauransu? - Sai nace masa a'a bata fara ba. - Sai yace min 'to wai me take jira har yanzu bata fara kai

SHELAR FUNTUA FAƊAKARWA GA MUSULMIN NIGERIYA

Image
SHELAR FUNTUA: FADAKARWA GA MUSULMIN NIJERIYA Bana shekaru 40 daidai kenan da Shaikh Ibraheem Zakzaky ya gabatar da wannan jawabin na shelanta bara'a ga tsarin da ya sabawa na Allah da jaddada wila'a ga Allah da addininsa. Shaikh Zakzaky Ya yi jawabin nan a garin Funtua a watan April 1980. Kuma tun wancan shekarun har zuwa yau a kan wannan Shaikh Zakzaky yake, bai sauya ba, kuma akan wannan komai da ke samunsa ke samunsa. A kan wannan yake kira, kuma a kansa yake bukatar a amsa masa. Akansa ya tsayu, a kansa kuma yake fatan mabiyansa mu tsayu ba wani sirki. Ga jawabin nan: FADAKARWA GA MUSULMIN NIJERIYA Da sunan Allah mai murkushe azzalumai. Ya ’Yan uwa Musulmi maza da mata! Assalamu alaikum wa rahamatullah. An ruwaito cewa Sayyidina Ali Dan Abu Talib (Allah ya yarda da shi) ya ce: “Ya ku mutane, hakika Manzon Allah ya ce; ‘idan wani ya ga wata gwamnati ta mai da zalunci kiranta, ta keta haddodin Allah, ta shuka kiyayya ga sunnar Manzon Allah, tana aikata barna da zal

TAKAITACCEN TARIHIN JANAR QASIM SULAIMANI

Image
An haifi Laftanar Janar Ƙasim Sulaimani ne a shekarar 1957 a ƙauyen Ƙanat-e Malek da ke lardin Kerman na ƙasar Iran. A lokacin samartakarsa ya bar garin na su in da ya koma garin Kerman da zama inda a nan ya yi karatu da kuma ci gaba da gudanar da wasu ayyuka na hannu musamman gine-gine don samun abin rayuwa, kamar yadda kuma a can ne ya dinga halartar lakcocin wani malami da yake zuwa yankin da suke mai suna Hojjat Kamyab, wanda kuma ya kasance ɗaya daga cikin mabiya marigayi Imam Khumaini (r.a). Shahid Janar Ƙasim Sulaimani ya shiga cikin dakarun kare juyin juya halin Musulunci (IRGC) ne a shekarar 1979 bayan nasarar juyin juya halin Musulunci a ƙasar Iran da kuma kafa dakarun da marigayi Imam Khumaini yayi. Bayan wani lokaci ya samu horo da kuma ƙwarewa cikin wannan aiki na soji. A shekarar 1980 lokacin da Saddam Husain ya ƙaddamar da yaƙi kan Iran wanda ya ɗau shekaru takwas ana yi, Janar Sulaimani ya shiga cikin yaƙin inda ya jagoranci wasu dakarun sojoji daga lardin Kerman w